Home General Hukumar KANSIEC ta sauya ranar zabe a jihar Kano

Hukumar KANSIEC ta sauya ranar zabe a jihar Kano

Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano, KANSIEC ta sanar da sauya ranar gudanar da zaben kananan hukumomi zuwa 26 ga watan Oktoba.

shugaban hukumar, Farfesa Sani Lawan Malumfashi, ne ya bayyana hakan a yayin taron manema labarai daya gudana ranar Juma’a a Kano, inda ya ce hukumar ta dauki wannan matakin ne duba da hukuncin da kotun koli ta yi na bai wa kananan hukumomi ‘yanci.

Tun da fari dai hukumar ta sanka ranar 30 ga watan Nuwamba domin gudanar da zaben.

Malumfashi, ya ce bisa gyaran da aka yi, a yanzu za a fara yakin neman zabe daga 1 ga watan Satumba zuwa karfe 12 na daren 26 ga watan Oktoba.

Sannan ya kara da cewa za a gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyu daga 3 ga watan Satumba zuwa 26 ga watan. haka kuma za a sanar da sakamakon zabe a ranar Lahadi 27 ga watan Oktoba.

daga bisani yace hukumar ta ware ranar 9 ga watan Nuwamba domin zaben cike gurbi idan akwai bukatar hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp