Home General Yadda biyan ƴanbindiga kuɗin fansa ke illa ga tsaron Najeriya

Yadda biyan ƴanbindiga kuɗin fansa ke illa ga tsaron Najeriya

Afghan military personnel walk near the airport during fighting between Taliban militants and Afghan security forces in Kunduz on October 1, 2015. Afghan forces pushed into the centre of Kunduz on October 1, triggering pitched gunfights as they sought to flush out Taliban insurgents who held the northern city for three days in a stinging blow to the country's NATO-trained military The stunning fall of the provincial capital, even temporarily, highlighted the stubborn insurgency's potential to expand beyond its rural strongholds in the south of the country Afghan forces, hindered by the slow arrival of reinforcements but backed by NATO special forces and US air support, struggled to regain control of the city after three days of heavy fighting. AFP PHOTO / Wakil Kohsar

Wani rahoto na Kamfanin SB Morgen da ke sa ido kan harkokin tsaro a Yammacin Afirka, ya ce masu garkuwa da mutane a Najeriya sun nemi kusan naira biliyan 10.9 a matsayin kudin fansa daga iyalan wadanda suka sace daga watan Junin 2023 zuwa Yulin 2024.

Rahoton kamfanin wanda takensa shi ne yadda satar mutane ta zama kasuwanci a Najeriya, ya ce daga cikin kudaden da aka nema, ƴanbindigar sun yi nasarar karɓar kimanin naira biliyan daya.

Kusan kullum, ‘yan Najeriya musamman mazauna yankin arewa maso yamma, na cikin fargabar sacewa ko kisa daga ‘yan fashin daji da ke kai hare-hare a kullum.

Rahoton ya ce mutum 7,568 ne aka sace a sassan Najeriya tsakanin Yunin 2023 zuwa Yulin 2024.

Ƴanbindigar da ke satar mutane domin kuɗin fansa sun ƙunshi mayaƙan Boko Haram da ke arewa maso gabashi, da ƴanbindiga da ke cin karensu ba babbaka a arewa maso tsakiya da arewa maso yammaci da kuma ayyukan masu barazanar ɓallewa daga ƙasar a kudu maso kudu.

Rahoton ya ce jihohin Zamfara da Katsina da Kaduna da ke shiyar arewa maso yammaci matsalar ta satar mutane domin kuɗin fansa ta fi yin ƙamari.

Kuma a jihohin guda uku ne aka fi satar kisan mutane, a cewar rahoton na SB Morgen.

Rahoton ya ce a shekarar 2024 kaɗai, an kashe mutum 1,056 ta sanadin ƙoƙarin sace su, yayin da kuma aka saci mutum 1,130.

Rahoton ya ce wani abu da ke ƙara haifar da barazana shi ne yadda ƴanbindigar ke saɓa alƙawali, inda suke kashe mutane duk da an biya su kuɗin fansa.

Ko a makon da ya gabata ƴanbindiga sun kashe Sarkin Gobir na Gatawa Isa Bawa, bayan kwashe makonni a hannunsu suna garkuwa da shi, lamarin da ya girgiza ƴan Najeriya.

Masana tsaro irinsu Malam Kabiru Adamu shugaban kamfanin Beacon Consulting ya ce dole akwai waɗanda ke da alaƙa da ƴanbindigar da suke aiki tare da ke taimaka masu a harkar satar mutane domin karɓar kuɗin fansa.

“duk lokacin da aka ce an samu matsala ta tsaro irin wannan, da wahala ka ga cewa shi ainihin wanda yake yi a ce shi kaɗai ne dole akwai waɗanda ke taimaka masa,” in ji masanin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp