Home General Yadda biyan ƴanbindiga kuɗin fansa ke illa ga tsaron Najeriya

Yadda biyan ƴanbindiga kuɗin fansa ke illa ga tsaron Najeriya

'Yan Ta'adda

Wani rahoto na Kamfanin SB Morgen da ke sa ido kan harkokin tsaro a Yammacin Afirka, ya ce masu garkuwa da mutane a Najeriya sun nemi kusan naira biliyan 10.9 a matsayin kudin fansa daga iyalan wadanda suka sace daga watan Junin 2023 zuwa Yulin 2024.

Rahoton kamfanin wanda takensa shi ne yadda satar mutane ta zama kasuwanci a Najeriya, ya ce daga cikin kudaden da aka nema, ƴanbindigar sun yi nasarar karɓar kimanin naira biliyan daya.

Kusan kullum, ‘yan Najeriya musamman mazauna yankin arewa maso yamma, na cikin fargabar sacewa ko kisa daga ‘yan fashin daji da ke kai hare-hare a kullum.

Rahoton ya ce mutum 7,568 ne aka sace a sassan Najeriya tsakanin Yunin 2023 zuwa Yulin 2024.

Ƴanbindigar da ke satar mutane domin kuɗin fansa sun ƙunshi mayaƙan Boko Haram da ke arewa maso gabashi, da ƴanbindiga da ke cin karensu ba babbaka a arewa maso tsakiya da arewa maso yammaci da kuma ayyukan masu barazanar ɓallewa daga ƙasar a kudu maso kudu.

Rahoton ya ce jihohin Zamfara da Katsina da Kaduna da ke shiyar arewa maso yammaci matsalar ta satar mutane domin kuɗin fansa ta fi yin ƙamari.

Kuma a jihohin guda uku ne aka fi satar kisan mutane, a cewar rahoton na SB Morgen.

Rahoton ya ce a shekarar 2024 kaɗai, an kashe mutum 1,056 ta sanadin ƙoƙarin sace su, yayin da kuma aka saci mutum 1,130.

Rahoton ya ce wani abu da ke ƙara haifar da barazana shi ne yadda ƴanbindigar ke saɓa alƙawali, inda suke kashe mutane duk da an biya su kuɗin fansa.

Ko a makon da ya gabata ƴanbindiga sun kashe Sarkin Gobir na Gatawa Isa Bawa, bayan kwashe makonni a hannunsu suna garkuwa da shi, lamarin da ya girgiza ƴan Najeriya.

Masana tsaro irinsu Malam Kabiru Adamu shugaban kamfanin Beacon Consulting ya ce dole akwai waɗanda ke da alaƙa da ƴanbindigar da suke aiki tare da ke taimaka masu a harkar satar mutane domin karɓar kuɗin fansa.

“duk lokacin da aka ce an samu matsala ta tsaro irin wannan, da wahala ka ga cewa shi ainihin wanda yake yi a ce shi kaɗai ne dole akwai waɗanda ke taimaka masa,” in ji masanin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp