Home General Gwamnatin Kano ta fara daga darajar kananan Asibitocin jihar

Gwamnatin Kano ta fara daga darajar kananan Asibitocin jihar

Gwamnan Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya bada Umarnin daga darajar karamin asibitin da ke karamar hukumar Albasu zuwa babban Asibiti domin ci gaba da Inganta harkokin kiwon lafiya a karkara

Gwamnan ya bayyana hakan ne Lokacin da ya Kai ziyara duba aikin hanyar kilomita biyar-biyar a yankin.

Hakaza Gwamnan ya bawa ma,aikar ayyuka da gidaje ta Jihar umarnin magance matsalar zai-zayar kasa da ke damun kauyen Hamdullahi na karamar hukumar.

Har ila yau Gwamnan ya bada Umarni fara gyara hanyar da ta tashi daga kwanar Albasu zuwa cikin gari.

daga bisani Gwamnan ya Kai ziyarar gani da ido makarantar kwana ta yammata da ke garin Albasu a wani mataki na fara shirye shiryen sake bude ta domin ci gaba da karatu.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp