Home General CISLAC ta zargi CBN da facaka da kudin Nijeriya

CISLAC ta zargi CBN da facaka da kudin Nijeriya

Ƙungiyar CISLAC mai sanya idanu kan ayyukan majalisa a Najeriya ta yi tur da matakin Babban Bankin ƙasar, CBN na zargin facaka da kuɗaɗe masu yawa kan shugabaninsa, lokacin da ake fama da matsalar yunwa da hauhawar farashin kayayyaki.

Ta cikin wata sanarwa da ta fitar mai ɗauke da sa hannun babban daraktanta Auwal Musa Rafsanjani, ƙungiyar ta ce an kashe kuɗaɗen ne kan shugaban bankin Yemi Cardoso da wasu mataimakansa huɗu.

CISLAC ta yi iƙirarin cewa Cardoso da mataimakansa da Majalisar Dattijai ta amince da naɗinsu a watan Satumbar 2023, sun kashe wa kansu naira biliyan 10 wajen sayan motoci masu sulke.

Daga bayanan da CISLAC ta samu ta ce “Mista Cardoso ya bayyana cewa ya saya wa kansa da mataimakansa motoci ƙirar Lexus LX 600 2023. Mataimakan nasa sun haɗa da Emem Usoro da Philip Ikeazor da Bala Bello da kuma Sani Abdullahi.

Majiyar CISLAC daga CBN ta shaida cewa Cardoso ya saya wa kansa wasu motoci biyu ƙirar SUV da zai riƙa amfani da su a Legas da Abuja duk da cewa akwai motoci masu sulke a tawagarsa da yake tafiya da su kusan koda yaushe.

Ƙungiyar ta kuma yi zargin Mista Cardoso ya sayi motoci ƙirar Toyota Camry sabbi guda 20 kan kuɗi naira miliyan 85 kowacce ɗaya, ya kuma raba su ga mambobin kwamitin amintattu na CBN.

Wani rahoton da CISLAC ta samu daga cikin CBN ya ce gwamnan bankin da mataimakansa sun ƙara wa kansu kudin alawus na gida zuwa kusan naira biliyan ɗaya a shekara ɗaya, duk da cewa suna zaune ne a gidajen gwamnati na alfarma da ke Maitama a Abuja.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp