Home General Gwamnan Kano ya kwace kwangilar Titin Garko mai tsawon kilomi 5

Gwamnan Kano ya kwace kwangilar Titin Garko mai tsawon kilomi 5

Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya ziyarci Dam din Kafinchiri a karamar hukumar Garko, domin ganin yadda aiki ke gudana, wanda aka bayar da shi a yunkurin kawo sauyi a fannin noma a jihar.

Wannan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar ranar Lahadi.

Sanarwar tace aikin, wanda darajarsa ta kai Naira biliyan 2.5, an yi shi ne da nufin bunkasa noman rani da damina, da inganta samar da abinci, da kuma bunkasa tattalin arzikin jihar.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya jaddada muhimmancin aikin noman na Kafinchiri, inda ya bayyana hakan a matsayin wani muhimmin bangare na kokarin gwamnatinsa na bunkasa noma a jihar Kano.

Ya bukaci mazauna garin Garko da kewaye da su yi amfani da damar da aikin zai bayar domin inganta tattalin arzikin su da jihar baki daya.

A wani labarin kuma, Gwamnan ya sanar da kwace kwangilar aikin hanyar karamar hukumar Garko mai tsawon kilomita biyar saboda gazawar dan kwangilar na dawowa bakin aiki.

Ya ba da tabbacin cewa nan ba da jimawa ba za a baiwa wani mai kwazo kwangilar aikin don tabbatar da kammala aikin a kan kari.

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya kuma kuduri aniyar samar da cibiyar lafiya ta zamani a garin Garko, da nufin kusantar da harkokin kiwon lafiya ga jama’a.

Ya nuna jin dadinsa bisa goyon bayan da al’ummar yankin suke ba shi tare da jaddada aniyar gwamnatinsa na ci gaba gudanar da aiyukan cigaba a jihar .

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp