Home General Hukumar KANSIEC ta sauya ranar zabe a jihar Kano

Hukumar KANSIEC ta sauya ranar zabe a jihar Kano

Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano, KANSIEC ta sanar da sauya ranar gudanar da zaben kananan hukumomi zuwa 26 ga watan Oktoba.

shugaban hukumar, Farfesa Sani Lawan Malumfashi, ne ya bayyana hakan a yayin taron manema labarai daya gudana ranar Juma’a a Kano, inda ya ce hukumar ta dauki wannan matakin ne duba da hukuncin da kotun koli ta yi na bai wa kananan hukumomi ‘yanci.

Tun da fari dai hukumar ta sanka ranar 30 ga watan Nuwamba domin gudanar da zaben.

Malumfashi, ya ce bisa gyaran da aka yi, a yanzu za a fara yakin neman zabe daga 1 ga watan Satumba zuwa karfe 12 na daren 26 ga watan Oktoba.

Sannan ya kara da cewa za a gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyu daga 3 ga watan Satumba zuwa 26 ga watan. haka kuma za a sanar da sakamakon zabe a ranar Lahadi 27 ga watan Oktoba.

daga bisani yace hukumar ta ware ranar 9 ga watan Nuwamba domin zaben cike gurbi idan akwai bukatar hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp