Home General Hukumar KANSIEC ta sauya ranar zabe a jihar Kano

Hukumar KANSIEC ta sauya ranar zabe a jihar Kano

Hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano, KANSIEC ta sanar da sauya ranar gudanar da zaben kananan hukumomi zuwa 26 ga watan Oktoba.

shugaban hukumar, Farfesa Sani Lawan Malumfashi, ne ya bayyana hakan a yayin taron manema labarai daya gudana ranar Juma’a a Kano, inda ya ce hukumar ta dauki wannan matakin ne duba da hukuncin da kotun koli ta yi na bai wa kananan hukumomi ‘yanci.

Tun da fari dai hukumar ta sanka ranar 30 ga watan Nuwamba domin gudanar da zaben.

Malumfashi, ya ce bisa gyaran da aka yi, a yanzu za a fara yakin neman zabe daga 1 ga watan Satumba zuwa karfe 12 na daren 26 ga watan Oktoba.

Sannan ya kara da cewa za a gudanar da zaben fidda gwani na jam’iyyu daga 3 ga watan Satumba zuwa 26 ga watan. haka kuma za a sanar da sakamakon zabe a ranar Lahadi 27 ga watan Oktoba.

daga bisani yace hukumar ta ware ranar 9 ga watan Nuwamba domin zaben cike gurbi idan akwai bukatar hakan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp