Home General Matatar Dangote za ta samar da lita man fetur miliyan 25 a...

Matatar Dangote za ta samar da lita man fetur miliyan 25 a kowace rana – NMDRA

Hukumar da ke sanya idanu kan harkokin man fetur ta Nijeriya (NMDPRA) ta sanar da cewa sabuwar matatar mai ta Dangote za ta fara samar da lita miliyan 25 na man fetur a kowace rana ga kasuwannin Nijeriya a cikin watan Satumbar da muke ciki.

Ana sa ran adadin man zai ƙaru zuwa lita miliyan 30 a kowace rana daga watan Oktoba.

A wata sanarwa da hukumar ta wallafa a shafin sada zumuntarta na X ta bayyana cewa, a wani taro da suka yi a Abuja ranar Talata, NMDPRA da Kamfanin NNPCL sun amince da fara sayar da ɗanyen mai ga matatar Dangote da kuɗin ƙasar wato Naira.

Bayan shafe sama da shekara guda da taƙaddamar da aikinta a watan Mayun 2023, matatar Dangote, a ranar Talata, ta fara fitar da man fetur ɗin.

A jiya ne dai kamfanin NNPCL ta ƙara farashin man fetur daga naira 617 zuwa naira 897.

Aliko Dangote ya ce da zarar kamfaninsa ya kammala shirye-shirye da NNPCL, man fetur na kamfanin zai shiga kasuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp