Home General Gwamnonin PDP na son jami’an tsaro su ɗauki mataki kan Wike

Gwamnonin PDP na son jami’an tsaro su ɗauki mataki kan Wike

Ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ta buƙaci jami’an tsaron Nijeriya su ɗauki mataki kan ‘barazanar’ da suka ce Ministan Abuja, Nyesom Wike ya yi musu.

A ƙarshen makon a ya gabata ne dai tsohon gwamnan na jihar Rivers ya yi barazanar haifar da rikicin siyasa a jihohin gwamnonin jam’iyyar, matsawar suka ci gaba da sa baki kan rikicin siyasar jihar Rivers.

”Na ji wasu gwamnoni da suka ce za su ƙwace jam’iyyarmu don miƙa wa wani, Ina tausaya wa waɗannan gwamnoni, saboda zan kunno musu wutar da ba za su iya kashe ta ba a jihohinsu”, in ji Mista Wike.

To sai dai cikin sanarwar da daraktan ƙungiyar gwamnonin PDPn, Emmanuel Agbo, ya fitar ƙungiyar ta ce babu wanda ya fi ƙarfin doka sannan ta buƙaci jami’an tsaro su ɗauki mataki kan kalaman ministan, kamar yadda gidan Talbijin na Channels ya ruwaito.

“Ƙungiyarmu na kira da shugabannin hukumomin tsaro na ƙasar nan su ɗauki mataki kan kalaman ministan da ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali da ƙoƙarin haifar da fiitina a jihohin, saboda babu wanda ya fi ƙarfin doka”, in ji sanarwar.

Gwamnonin na PDP sun kuma ce kalaman na mista Wike ba abu ne da za a lamunta ba saboda yadda suke barazana ga zaman lafiyar ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp