Home General Gwamnonin PDP na son jami’an tsaro su ɗauki mataki kan Wike

Gwamnonin PDP na son jami’an tsaro su ɗauki mataki kan Wike

Ƙungiyar gwamnonin jam’iyyar PDP ta buƙaci jami’an tsaron Nijeriya su ɗauki mataki kan ‘barazanar’ da suka ce Ministan Abuja, Nyesom Wike ya yi musu.

A ƙarshen makon a ya gabata ne dai tsohon gwamnan na jihar Rivers ya yi barazanar haifar da rikicin siyasa a jihohin gwamnonin jam’iyyar, matsawar suka ci gaba da sa baki kan rikicin siyasar jihar Rivers.

”Na ji wasu gwamnoni da suka ce za su ƙwace jam’iyyarmu don miƙa wa wani, Ina tausaya wa waɗannan gwamnoni, saboda zan kunno musu wutar da ba za su iya kashe ta ba a jihohinsu”, in ji Mista Wike.

To sai dai cikin sanarwar da daraktan ƙungiyar gwamnonin PDPn, Emmanuel Agbo, ya fitar ƙungiyar ta ce babu wanda ya fi ƙarfin doka sannan ta buƙaci jami’an tsaro su ɗauki mataki kan kalaman ministan, kamar yadda gidan Talbijin na Channels ya ruwaito.

“Ƙungiyarmu na kira da shugabannin hukumomin tsaro na ƙasar nan su ɗauki mataki kan kalaman ministan da ke barazana ga zaman lafiya da kwanciyar hankali da ƙoƙarin haifar da fiitina a jihohin, saboda babu wanda ya fi ƙarfin doka”, in ji sanarwar.

Gwamnonin na PDP sun kuma ce kalaman na mista Wike ba abu ne da za a lamunta ba saboda yadda suke barazana ga zaman lafiyar ƙasa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp