Home General Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Daraktan Kiwon Lafiya a Matakin Farko na Jihar Jigawa, Dr. Shehu Sambo, ya ce adadin rigakafi ya karu daga kashi bakwai cikin dari a shekarar 2016 zuwa kashi 49 cikin dari a shekarar 2021.

Sambo ya bayyana hakan ne yau Laraba a Dutse, yayin taron tattaunawa da manema labarai da kaddamar da gangamin kwanaki biyu kan “Karfi da Inganta Tsarin PHC: Yarjejeniyar UNICEF kan PHC a Jihar Jigawa,” wanda UNICEF da Hukumar Kula da Hakkokin Yara da kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya suka shirya.

Ya ce an sanya hannu kan yarjejeniyar a shekarar 2022 tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Gwamnatin Tarayya, Kungiyar Gwamnonin Najeriya, GAVI, da UNICEF don inganta rigakafi a kai a kai, inganta tsarin PHC, da rage yawan mace-macen mata da yara.

Sambo ya bayyana cewa daya daga cikin dabarun da aka dauka don karfafa yin rigakafi shine karfafa kwamitin kula da aiyukan PHC ta hanyar kyakkyawan shugabanci da jagoranci.

Haka kuma ya bayyana cewa kudaden da aka samu daga GAVI sun basu damar samun karin kudade don daukar ma’aikatan ungozoma da horar da ma’aikatan lafiya a matakin farko don samar da aiyukan da ake bukata ga dukkan wuraren da ke da wahalar isa a fadin jihar.

Ya ce, “Kafin wannan yarjejeniyar, muna da kimanin ungozoma 120 a ɓangaren PHC, amma yanzu, mun dauki fiye da ungozoma 300 don kara ma’aikatan da muke da su. Yanzu haka, muna da fiye da ungozoma 500 da ke aiki a sashen PHC na Jihar Jigawa.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp