Home General Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Daraktan Kiwon Lafiya a Matakin Farko na Jihar Jigawa, Dr. Shehu Sambo, ya ce adadin rigakafi ya karu daga kashi bakwai cikin dari a shekarar 2016 zuwa kashi 49 cikin dari a shekarar 2021.

Sambo ya bayyana hakan ne yau Laraba a Dutse, yayin taron tattaunawa da manema labarai da kaddamar da gangamin kwanaki biyu kan “Karfi da Inganta Tsarin PHC: Yarjejeniyar UNICEF kan PHC a Jihar Jigawa,” wanda UNICEF da Hukumar Kula da Hakkokin Yara da kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya suka shirya.

Ya ce an sanya hannu kan yarjejeniyar a shekarar 2022 tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Gwamnatin Tarayya, Kungiyar Gwamnonin Najeriya, GAVI, da UNICEF don inganta rigakafi a kai a kai, inganta tsarin PHC, da rage yawan mace-macen mata da yara.

Sambo ya bayyana cewa daya daga cikin dabarun da aka dauka don karfafa yin rigakafi shine karfafa kwamitin kula da aiyukan PHC ta hanyar kyakkyawan shugabanci da jagoranci.

Haka kuma ya bayyana cewa kudaden da aka samu daga GAVI sun basu damar samun karin kudade don daukar ma’aikatan ungozoma da horar da ma’aikatan lafiya a matakin farko don samar da aiyukan da ake bukata ga dukkan wuraren da ke da wahalar isa a fadin jihar.

Ya ce, “Kafin wannan yarjejeniyar, muna da kimanin ungozoma 120 a ɓangaren PHC, amma yanzu, mun dauki fiye da ungozoma 300 don kara ma’aikatan da muke da su. Yanzu haka, muna da fiye da ungozoma 500 da ke aiki a sashen PHC na Jihar Jigawa.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp