Home General Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Daraktan Kiwon Lafiya a Matakin Farko na Jihar Jigawa, Dr. Shehu Sambo, ya ce adadin rigakafi ya karu daga kashi bakwai cikin dari a shekarar 2016 zuwa kashi 49 cikin dari a shekarar 2021.

Sambo ya bayyana hakan ne yau Laraba a Dutse, yayin taron tattaunawa da manema labarai da kaddamar da gangamin kwanaki biyu kan “Karfi da Inganta Tsarin PHC: Yarjejeniyar UNICEF kan PHC a Jihar Jigawa,” wanda UNICEF da Hukumar Kula da Hakkokin Yara da kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya suka shirya.

Ya ce an sanya hannu kan yarjejeniyar a shekarar 2022 tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Gwamnatin Tarayya, Kungiyar Gwamnonin Najeriya, GAVI, da UNICEF don inganta rigakafi a kai a kai, inganta tsarin PHC, da rage yawan mace-macen mata da yara.

Sambo ya bayyana cewa daya daga cikin dabarun da aka dauka don karfafa yin rigakafi shine karfafa kwamitin kula da aiyukan PHC ta hanyar kyakkyawan shugabanci da jagoranci.

Haka kuma ya bayyana cewa kudaden da aka samu daga GAVI sun basu damar samun karin kudade don daukar ma’aikatan ungozoma da horar da ma’aikatan lafiya a matakin farko don samar da aiyukan da ake bukata ga dukkan wuraren da ke da wahalar isa a fadin jihar.

Ya ce, “Kafin wannan yarjejeniyar, muna da kimanin ungozoma 120 a ɓangaren PHC, amma yanzu, mun dauki fiye da ungozoma 300 don kara ma’aikatan da muke da su. Yanzu haka, muna da fiye da ungozoma 500 da ke aiki a sashen PHC na Jihar Jigawa.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp