Home General Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Gwamnatin Jigawa tace Adadin Karɓar Rigakafi Ya Ƙaru Zuwa Kashi 49%

Daraktan Kiwon Lafiya a Matakin Farko na Jihar Jigawa, Dr. Shehu Sambo, ya ce adadin rigakafi ya karu daga kashi bakwai cikin dari a shekarar 2016 zuwa kashi 49 cikin dari a shekarar 2021.

Sambo ya bayyana hakan ne yau Laraba a Dutse, yayin taron tattaunawa da manema labarai da kaddamar da gangamin kwanaki biyu kan “Karfi da Inganta Tsarin PHC: Yarjejeniyar UNICEF kan PHC a Jihar Jigawa,” wanda UNICEF da Hukumar Kula da Hakkokin Yara da kuma Ma’aikatar Yaɗa Labarai ta Tarayya suka shirya.

Ya ce an sanya hannu kan yarjejeniyar a shekarar 2022 tsakanin Gwamnatin Jihar Jigawa, Gwamnatin Tarayya, Kungiyar Gwamnonin Najeriya, GAVI, da UNICEF don inganta rigakafi a kai a kai, inganta tsarin PHC, da rage yawan mace-macen mata da yara.

Sambo ya bayyana cewa daya daga cikin dabarun da aka dauka don karfafa yin rigakafi shine karfafa kwamitin kula da aiyukan PHC ta hanyar kyakkyawan shugabanci da jagoranci.

Haka kuma ya bayyana cewa kudaden da aka samu daga GAVI sun basu damar samun karin kudade don daukar ma’aikatan ungozoma da horar da ma’aikatan lafiya a matakin farko don samar da aiyukan da ake bukata ga dukkan wuraren da ke da wahalar isa a fadin jihar.

Ya ce, “Kafin wannan yarjejeniyar, muna da kimanin ungozoma 120 a ɓangaren PHC, amma yanzu, mun dauki fiye da ungozoma 300 don kara ma’aikatan da muke da su. Yanzu haka, muna da fiye da ungozoma 500 da ke aiki a sashen PHC na Jihar Jigawa.”

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp