Gwamnatin Nijeriya ta bar Jakki tana Tukan Taiki – Atiku

Tsohon mataimakain shugaban kasa kuma Jagoran adawar Najeriya, Atiku Abubakar, ya zargi gwamnatin ƙasar da mayar da hankali kan wasu abubuwa da ya kira marasa muhimmanci tare da yin watsi da matsala tsaro da ƙasar ke fama da ita.

Cikin wani saƙo da ya wallafa a shafinsa na X, tsohon ɗan takarar shugaba ƙasar na jam’iyyar PDP ya yi Allah wadai da harin da mayaƙan Boko Haram suka kai jihar Yobe, da ya yi sanadin mutuwar mutane da dama.

Ya kuma yi tsokaci kan yawan tashe-tashen hankula da ke ci gaba da faruwa a jihohin Katsina da Sokoto da sauran sassan Arewa.

Atiku ya zargi gwamnati da cewa ta fi damuwa da kama masu zanga-zanga, maimakon magance matsalar rashin tsaro.

“Duk da mummunan zubar da jini da aka yi a Yobe, wanda ya yi sanadin mutuwar mutane da dama, da kuma ɓarnar da aka yi a ƙauyuka da dama a Katsina da Sakoto, da sauran garuruwan da ke yankin arewa maso yamma da arewa ta tsakiya, da dukkan alamu gwamnati ta fi mayar da hankali kan ayyukanta da sauran abubuwa da ba zu da muhimmanci.” in ji Atiku.

Atiku ya kuma yi nuni da tashe-tashen hankulan da ‘yan Boko Haram ke haifarwa da rigingimun siyasa a kudu.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1187 days 17 hours 57 minutes 44 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1169 days 19 hours 39 minutes 9 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com