Home General Hanyoyin Samun Shinkafar Gwamnati mai rahusa a Nijeriya

Hanyoyin Samun Shinkafar Gwamnati mai rahusa a Nijeriya

Gwamnatin Najeriya ta ce ma’aikatan gwamnati waɗanda suke da lambar ɗan ƙasa ta NIN ne za a bai wa damar sayen shinkafar da gwamnatin za ta sayar a farashi mai rahusa.

Ministan Noma, Abubakar Kyari ne ya sanar da hakan, inda ya ce hakan zai taimaka wajen rage ci da zuci da kuma saye abincin a kasuwa da ma rage tsadar abincin a kasuwannin Najeriya.

Abubakar Kyari ya ce a ƙarƙashin tsarin, “buhu ɗaya kawai mutum zai samu.”

Ya ce buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50 za a sayar a farashin Naira 40,000 a cikin shirin gwamnatin na rage raɗaɗin tsadar kayan masarufi.

Gidan talbijin na Channels ya ambato ministan na cewa sai wanda ya mallaki shaidar ɗan ƙasa wato NIN ne kawai zai samu damar sayen shinkafar.

Ya ce an saki tan 42,000 na kayan masarufi, da kuma tan 30,000 na shinkafa wanda za a sayar wa ƴan Najeriya.

Ya ce ana sa ran fitar da abincin na gwamnati zai sa farashin abincin ya sauka a kasuwanni.

Darakta, ɓangaren abinci da tsare-tsaren tanadi na ma’aikatar, Haruna Sule Abutu ya bayyana sharaɗin da za a cika domin samun damar sayan abincin kamar haka:

  • Dole mutum ya mallaki lambar ɗan ƙasa ta NIN
  • Lambar waya
  • Rajista da IPPIS idan ma’aikacin gwamnati ne

Ya ce idan mutum ya zo wurin sayar da shinkafar da abubuwa guda uku, za a tantance shi, sai a ba shi wata lamba da rasitin da mutum zai kai wajen da ake karɓa ya ɗauko shinkafarsa.

Ya ƙara da cewa a jikin rasit ɗin kowa akwai lokaci da wajen da zai je ya ɗauki tasa shinkafar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp