Mamakon ruwan sama na kwanaki biyar zai haddasa ambaliya a jihohi 21 – NIMET

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta yi hasashen cewa mamakon ruwan sama da za a yi kwana biyar ana yi, zai janyo ambaliyar ruwa a wurare 123 na jihohi 21 na ƙasar.

Rahoton ya bayyana jihohin Benue da Kogi da Anambra da Delta da Rivers da Imo da Bayelsa a matsayin jihohin da iftila’in zai fi ƙamari.

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito cewa wani rahoto da hukumar kare muhalli ta fitar ya yi kira ga mazauna waɗanann jihohi riƙa sanya idanu tare da lura da al’amura.

Gwamnatin ta kuma bayyana cewa yankuna 123 ne za su iya fuskantar ambaliyar, wadda ake hasashen zai faru tsakanin 4 ga Satumba zuwa 8 ga Satumba.

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1462 days 18 hours 42 minutes 22 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1444 days 20 hours 23 minutes 47 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com