Home General Hanyoyin Samun Shinkafar Gwamnati mai rahusa a Nijeriya

Hanyoyin Samun Shinkafar Gwamnati mai rahusa a Nijeriya

Gwamnatin Najeriya ta ce ma’aikatan gwamnati waɗanda suke da lambar ɗan ƙasa ta NIN ne za a bai wa damar sayen shinkafar da gwamnatin za ta sayar a farashi mai rahusa.

Ministan Noma, Abubakar Kyari ne ya sanar da hakan, inda ya ce hakan zai taimaka wajen rage ci da zuci da kuma saye abincin a kasuwa da ma rage tsadar abincin a kasuwannin Najeriya.

Abubakar Kyari ya ce a ƙarƙashin tsarin, “buhu ɗaya kawai mutum zai samu.”

Ya ce buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50 za a sayar a farashin Naira 40,000 a cikin shirin gwamnatin na rage raɗaɗin tsadar kayan masarufi.

Gidan talbijin na Channels ya ambato ministan na cewa sai wanda ya mallaki shaidar ɗan ƙasa wato NIN ne kawai zai samu damar sayen shinkafar.

Ya ce an saki tan 42,000 na kayan masarufi, da kuma tan 30,000 na shinkafa wanda za a sayar wa ƴan Najeriya.

Ya ce ana sa ran fitar da abincin na gwamnati zai sa farashin abincin ya sauka a kasuwanni.

Darakta, ɓangaren abinci da tsare-tsaren tanadi na ma’aikatar, Haruna Sule Abutu ya bayyana sharaɗin da za a cika domin samun damar sayan abincin kamar haka:

  • Dole mutum ya mallaki lambar ɗan ƙasa ta NIN
  • Lambar waya
  • Rajista da IPPIS idan ma’aikacin gwamnati ne

Ya ce idan mutum ya zo wurin sayar da shinkafar da abubuwa guda uku, za a tantance shi, sai a ba shi wata lamba da rasitin da mutum zai kai wajen da ake karɓa ya ɗauko shinkafarsa.

Ya ƙara da cewa a jikin rasit ɗin kowa akwai lokaci da wajen da zai je ya ɗauki tasa shinkafar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp