Home General Hanyoyin Samun Shinkafar Gwamnati mai rahusa a Nijeriya

Hanyoyin Samun Shinkafar Gwamnati mai rahusa a Nijeriya

Gwamnatin Najeriya ta ce ma’aikatan gwamnati waɗanda suke da lambar ɗan ƙasa ta NIN ne za a bai wa damar sayen shinkafar da gwamnatin za ta sayar a farashi mai rahusa.

Ministan Noma, Abubakar Kyari ne ya sanar da hakan, inda ya ce hakan zai taimaka wajen rage ci da zuci da kuma saye abincin a kasuwa da ma rage tsadar abincin a kasuwannin Najeriya.

Abubakar Kyari ya ce a ƙarƙashin tsarin, “buhu ɗaya kawai mutum zai samu.”

Ya ce buhun shinkafa mai nauyin kilogiram 50 za a sayar a farashin Naira 40,000 a cikin shirin gwamnatin na rage raɗaɗin tsadar kayan masarufi.

Gidan talbijin na Channels ya ambato ministan na cewa sai wanda ya mallaki shaidar ɗan ƙasa wato NIN ne kawai zai samu damar sayen shinkafar.

Ya ce an saki tan 42,000 na kayan masarufi, da kuma tan 30,000 na shinkafa wanda za a sayar wa ƴan Najeriya.

Ya ce ana sa ran fitar da abincin na gwamnati zai sa farashin abincin ya sauka a kasuwanni.

Darakta, ɓangaren abinci da tsare-tsaren tanadi na ma’aikatar, Haruna Sule Abutu ya bayyana sharaɗin da za a cika domin samun damar sayan abincin kamar haka:

  • Dole mutum ya mallaki lambar ɗan ƙasa ta NIN
  • Lambar waya
  • Rajista da IPPIS idan ma’aikacin gwamnati ne

Ya ce idan mutum ya zo wurin sayar da shinkafar da abubuwa guda uku, za a tantance shi, sai a ba shi wata lamba da rasitin da mutum zai kai wajen da ake karɓa ya ɗauko shinkafarsa.

Ya ƙara da cewa a jikin rasit ɗin kowa akwai lokaci da wajen da zai je ya ɗauki tasa shinkafar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp