Ambaliyar ruwa ta mamaye kafancan

Wata mummunar ambaliyar ruwa ta raba mutane sama da 1,000 da muhallansu tare da hallaka yara biyu a Kafanchan da ke cikin ƙaramar hukumar Jema’a ta jihar Kaduna.

Misis Christy Usman, mataimakiyar shugabar ƙaramar hukumar Jema’a ce ta bayyana hakan, a wata ziyara da kwamitin da gwamnatin jihar Kaduna ta kafa domin nazari kan tasirin ambaliyar.

Ta ce ambaliyar wadda ta shafi “wasu sassan garin Kafanchan da Jagindi da Atuku da Aso da kuma Bade ta lalata gonaki da dama da kuma amfanin gona da darajarsu takai miliyoyin naira.”

“Ambaliyar ta yi illa ga tattalin arzikin ƙaramar hukumar Jema’a, amma Gwamnatin jihar ta dauki mataki cikin gaggawa.”

Kidnapped School Children

Yauri FGC Students, Kebbi
1190 days 9 hours 27 minutes 53 seconds,

Baptist School Students, Kaduna
1172 days 11 hours 9 minutes 18 seconds

Tegina Islamiya Pupils, Niger (Freed)
Spent 88 days from May 30, 2021 - August 26, 2021


Report By: PRNigeria.com

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com