Home General Tinubu ya taya al’ummar Maiduguri jimami kan iftila’in ambaliya

Tinubu ya taya al’ummar Maiduguri jimami kan iftila’in ambaliya

Bola Ahned Tinubu

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya nuna matukar damuwarsa game da ambaliyar ruwa da ta afku a wasu sassan Maiduguri babban birnin jihar Borno.

Wannan na kunshe ta cikin wata sanarwa da mai bai wa shugaban ƙasar shawara kan harkokin yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar.

Ambaliyar ruwan ita ce mafi muni a cikin shekarun baya-bayan nan da birnin ya fuskanta yayin da ta raba dubban mutane da muhallansu tare da yin ɓarna a karamar ofishin gidan waya da asibitin koyarwa na Maiduguri.

Tinubu ya jajanta wa gwamnati da al’ummar jihar, musamman waɗanda suka yi asara sakamakon bala’in da ambaliyar ruwan ta haddasa.

Tinubu ya kuma yi kira da a gaggauta kwashe mutane daga yankunan da abin ya shafa yayin da hukumomi ke ci gaba da tantance irin ɓarnar da ambaliyar ta yi.

Shugaban ya kuma umurci hukumar ba da agajin gaggawa ta ƙasa (NEMA) da ta taimaka wa waɗanda ambaliyar ta shafa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
https://nnn.ng/image-compressor/
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp