Home General Tinubu ya lashi takobin kawo karshen matsalar ambaliya a Nijeriya

Tinubu ya lashi takobin kawo karshen matsalar ambaliya a Nijeriya

NEMA
NEMA

Gwamantin tarayya Nijeriya ta lashi takobin kawo karshen ambaliyar ruwa a kasar Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayyana hakan ta bakin mataimakin sa Sanata Kashim Shettima a yayin da ya yi saukar gaggawa a birnin Maiduguri inda ya kai ziyarar gani-da- ido kan ambaliyar da ta rutsa da dubban mutane a garin.

Shattima ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta sa kafar wando-daya da kalubalen ambaliyar ruwa a kasar ta hanyar amfani da taswirar da za ta kawo maslaha ta dindindin.

Shettima, wanda ke jawabin cikin kaduwa a lokacin da yake tantance irin barnar da ambaliyar ta yi a garin Maiduguri, ya jajanta wa wadanda ibtila’in ya rutsa da su, inda ya bayyana musu cewa, shugaba Tinubu na tare da al’ummar da abin ya shafa, kuma gwamnatin tarayya za ta samar da dukkan abinda ake bukata domin tabbatar da tsaro da tallafawa mutanen da lamarin ya shafa.

Shettima ya danganta ambaliyar da ballewar madatsar ruwa ta Alau wanda ya ta’azzara lamarin har ya zarce irin wanda aka taba samu a baya. Sai dai kuma ya jaddada aniyarsa ta samar da mafita mai dorewa.

haka kuma ya yi kira da a ci gaba da wayar da kan al’umma kan karuwar barazanar da sauyin yanayi ke haifarwa tare da jaddada aniyar gwamnati ta magance wadannan kalubalen gaba daya.

Shettima, ya kuma yaba wa gwamnati da al’ummar jihar Borno bisa namijin kokarin da suka nuna wajen daukar matakan da suka dace akan lokaci tare da kai dauki ga al’ummar da lamarin ya shafa a cikin gaugawa.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp