Home General Ambaliya- Gwamnatin Nijeriya ta bude sansanonin ‘yan gudun hijira a Borno

Ambaliya- Gwamnatin Nijeriya ta bude sansanonin ‘yan gudun hijira a Borno

Rahotanni daga garin Maiduguri dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya ta tabbatar da cewa dubban mutane sun rasa matsugunansu yayin da Hukumar Kula da Gidajen Gyara Hali da trabiyya ta kasar ta sake kamo fursunoni uku da suka tsere bayan rugujewar kurkuku, sannan kashi 80% na dabbobin gidan zoo na Sanda Kyarimi sun mutu saboda ambaliyar ruwa mafi girma da aka samu a cikin shekaru 30 a Jihar.

Biyo bayan wannan mummunar annoba, Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi kira da a gaggauta kwashe al’ummomin da ambaliyar ta mamaye, duk da cewa baya kasar a yanzu.

Kimanin kashi 70% na birnin Maiduguri ya nutse cikin ruwa kamar yanda Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta bayyana, inda ruwa ya mamaye wurare da dama, ciki har da fadar Shehun Borno, Umar Ibn Garbai El-Kanemi, ofisoshin gwamnati, da wasu manyan wurare kamar kasuwar Monday Market da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri.

Kakakin NEMA, Manzo Ezekiel, ya bayyana cewa yankunan da aka saba ɗaukarsu a matsayin masu tudu suma sun nutse, wanda ya sa mutane da dama suka maƙale, yayin da wasu suka tashi da safe suka tarar suna cikin ruwa tsundum.

An bayyana cewa, sakamakon kwararar ruwan da ya biyo bayan fashewar Dam ɗin Alau, Maiduguri ta kasance ƙarkashin ruwa tun ƙarshen mako, inda NEMA ke ci gaba da gudanar da aikin ceto da bayar da tallafi ga mutanen da abin ya shafa.

Gwamnatin jihar ta Borno tare da haɗin gwiwar NEMA sun buɗe sansanoni guda uku don ba da mafaka ga ƴan gudun hijirar da ambaliyar ta raba da muhallansu.

Jami’an NEMA sun bayyana cewa sama da kashi 70% na mazauna Maiduguri sun rasa matsugunansu, tare da rufe makarantu da ofisoshin gwamnati sakamakon ambaliyar.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya isa Maiduguri don duba ɓarnar da ambaliyar ta yi, kuma ya umurci hukumomin gwamnati su hanzarta ba da taimako ga al’ummomin da abin ya shafa.

Hukumar Gidajen Gyara Hali ta Najeriya ta tabbatar da tserewar fursunoni sama da 200 daga kurkukun Maiduguri, amma a halin yanzu an sake kama uku daga cikinsu, yayin da ake ci gaba da neman sauran.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Rahoton ‘Yan Sanda ya Danganta Kashi 70% na Laifuka a Kano da Shaye-Shayen Miyagun Ƙwayoyi, Ya Gano Mutane 513 da ake Zargin Masu Safara NePantami Ya Samu Karfin Gwiwa Yayin Da Jama'a Ke Taya Shi Murna a Lokacin Ziyarar Ayyuka a GombeMa’aikatar Tsaro ta yi Karin Bayani Kan Yarjejeniyar Yaki da Ta’addanci da Turkiyya, ta Karyata Zargin ‘Jihadi’Tinubu na Neman Amincewar Majalisar Dattawa kan Sabon Rancen $516.3mGadon Mulkin Gombe: Wa Ke Jin Tsoron Tasirin Pantami Daga Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Masu Kera Makamai ba Bisa Ka'ida ba a Filato, Sun Kama Wadanda ake Zargi da Ta'addanci a NijarShin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa Malami
X whatsapp