Home General Ambaliya- Gwamnatin Nijeriya ta bude sansanonin ‘yan gudun hijira a Borno

Ambaliya- Gwamnatin Nijeriya ta bude sansanonin ‘yan gudun hijira a Borno

Rahotanni daga garin Maiduguri dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya ta tabbatar da cewa dubban mutane sun rasa matsugunansu yayin da Hukumar Kula da Gidajen Gyara Hali da trabiyya ta kasar ta sake kamo fursunoni uku da suka tsere bayan rugujewar kurkuku, sannan kashi 80% na dabbobin gidan zoo na Sanda Kyarimi sun mutu saboda ambaliyar ruwa mafi girma da aka samu a cikin shekaru 30 a Jihar.

Biyo bayan wannan mummunar annoba, Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi kira da a gaggauta kwashe al’ummomin da ambaliyar ta mamaye, duk da cewa baya kasar a yanzu.

Kimanin kashi 70% na birnin Maiduguri ya nutse cikin ruwa kamar yanda Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta bayyana, inda ruwa ya mamaye wurare da dama, ciki har da fadar Shehun Borno, Umar Ibn Garbai El-Kanemi, ofisoshin gwamnati, da wasu manyan wurare kamar kasuwar Monday Market da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri.

Kakakin NEMA, Manzo Ezekiel, ya bayyana cewa yankunan da aka saba ɗaukarsu a matsayin masu tudu suma sun nutse, wanda ya sa mutane da dama suka maƙale, yayin da wasu suka tashi da safe suka tarar suna cikin ruwa tsundum.

An bayyana cewa, sakamakon kwararar ruwan da ya biyo bayan fashewar Dam ɗin Alau, Maiduguri ta kasance ƙarkashin ruwa tun ƙarshen mako, inda NEMA ke ci gaba da gudanar da aikin ceto da bayar da tallafi ga mutanen da abin ya shafa.

Gwamnatin jihar ta Borno tare da haɗin gwiwar NEMA sun buɗe sansanoni guda uku don ba da mafaka ga ƴan gudun hijirar da ambaliyar ta raba da muhallansu.

Jami’an NEMA sun bayyana cewa sama da kashi 70% na mazauna Maiduguri sun rasa matsugunansu, tare da rufe makarantu da ofisoshin gwamnati sakamakon ambaliyar.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya isa Maiduguri don duba ɓarnar da ambaliyar ta yi, kuma ya umurci hukumomin gwamnati su hanzarta ba da taimako ga al’ummomin da abin ya shafa.

Hukumar Gidajen Gyara Hali ta Najeriya ta tabbatar da tserewar fursunoni sama da 200 daga kurkukun Maiduguri, amma a halin yanzu an sake kama uku daga cikinsu, yayin da ake ci gaba da neman sauran.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp