Home General Ambaliya- Gwamnatin Nijeriya ta bude sansanonin ‘yan gudun hijira a Borno

Ambaliya- Gwamnatin Nijeriya ta bude sansanonin ‘yan gudun hijira a Borno

Rahotanni daga garin Maiduguri dake jihar Borno a arewa maso gabashin Nijeriya ta tabbatar da cewa dubban mutane sun rasa matsugunansu yayin da Hukumar Kula da Gidajen Gyara Hali da trabiyya ta kasar ta sake kamo fursunoni uku da suka tsere bayan rugujewar kurkuku, sannan kashi 80% na dabbobin gidan zoo na Sanda Kyarimi sun mutu saboda ambaliyar ruwa mafi girma da aka samu a cikin shekaru 30 a Jihar.

Biyo bayan wannan mummunar annoba, Shugaban kasa Bola Tinubu ya yi kira da a gaggauta kwashe al’ummomin da ambaliyar ta mamaye, duk da cewa baya kasar a yanzu.

Kimanin kashi 70% na birnin Maiduguri ya nutse cikin ruwa kamar yanda Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Ƙasa (NEMA) ta bayyana, inda ruwa ya mamaye wurare da dama, ciki har da fadar Shehun Borno, Umar Ibn Garbai El-Kanemi, ofisoshin gwamnati, da wasu manyan wurare kamar kasuwar Monday Market da Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri.

Kakakin NEMA, Manzo Ezekiel, ya bayyana cewa yankunan da aka saba ɗaukarsu a matsayin masu tudu suma sun nutse, wanda ya sa mutane da dama suka maƙale, yayin da wasu suka tashi da safe suka tarar suna cikin ruwa tsundum.

An bayyana cewa, sakamakon kwararar ruwan da ya biyo bayan fashewar Dam ɗin Alau, Maiduguri ta kasance ƙarkashin ruwa tun ƙarshen mako, inda NEMA ke ci gaba da gudanar da aikin ceto da bayar da tallafi ga mutanen da abin ya shafa.

Gwamnatin jihar ta Borno tare da haɗin gwiwar NEMA sun buɗe sansanoni guda uku don ba da mafaka ga ƴan gudun hijirar da ambaliyar ta raba da muhallansu.

Jami’an NEMA sun bayyana cewa sama da kashi 70% na mazauna Maiduguri sun rasa matsugunansu, tare da rufe makarantu da ofisoshin gwamnati sakamakon ambaliyar.

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya isa Maiduguri don duba ɓarnar da ambaliyar ta yi, kuma ya umurci hukumomin gwamnati su hanzarta ba da taimako ga al’ummomin da abin ya shafa.

Hukumar Gidajen Gyara Hali ta Najeriya ta tabbatar da tserewar fursunoni sama da 200 daga kurkukun Maiduguri, amma a halin yanzu an sake kama uku daga cikinsu, yayin da ake ci gaba da neman sauran.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp