Home General Tinubu ya lashi takobin kawo karshen matsalar ambaliya a Nijeriya

Tinubu ya lashi takobin kawo karshen matsalar ambaliya a Nijeriya

NEMA
NEMA

Gwamantin tarayya Nijeriya ta lashi takobin kawo karshen ambaliyar ruwa a kasar Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayyana hakan ta bakin mataimakin sa Sanata Kashim Shettima a yayin da ya yi saukar gaggawa a birnin Maiduguri inda ya kai ziyarar gani-da- ido kan ambaliyar da ta rutsa da dubban mutane a garin.

Shattima ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta sa kafar wando-daya da kalubalen ambaliyar ruwa a kasar ta hanyar amfani da taswirar da za ta kawo maslaha ta dindindin.

Shettima, wanda ke jawabin cikin kaduwa a lokacin da yake tantance irin barnar da ambaliyar ta yi a garin Maiduguri, ya jajanta wa wadanda ibtila’in ya rutsa da su, inda ya bayyana musu cewa, shugaba Tinubu na tare da al’ummar da abin ya shafa, kuma gwamnatin tarayya za ta samar da dukkan abinda ake bukata domin tabbatar da tsaro da tallafawa mutanen da lamarin ya shafa.

Shettima ya danganta ambaliyar da ballewar madatsar ruwa ta Alau wanda ya ta’azzara lamarin har ya zarce irin wanda aka taba samu a baya. Sai dai kuma ya jaddada aniyarsa ta samar da mafita mai dorewa.

haka kuma ya yi kira da a ci gaba da wayar da kan al’umma kan karuwar barazanar da sauyin yanayi ke haifarwa tare da jaddada aniyar gwamnati ta magance wadannan kalubalen gaba daya.

Shettima, ya kuma yaba wa gwamnati da al’ummar jihar Borno bisa namijin kokarin da suka nuna wajen daukar matakan da suka dace akan lokaci tare da kai dauki ga al’ummar da lamarin ya shafa a cikin gaugawa.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp