Home General Tinubu ya lashi takobin kawo karshen matsalar ambaliya a Nijeriya

Tinubu ya lashi takobin kawo karshen matsalar ambaliya a Nijeriya

NEMA
NEMA

Gwamantin tarayya Nijeriya ta lashi takobin kawo karshen ambaliyar ruwa a kasar Shugaban kasa Bola Ahmad Tinubu ya bayyana hakan ta bakin mataimakin sa Sanata Kashim Shettima a yayin da ya yi saukar gaggawa a birnin Maiduguri inda ya kai ziyarar gani-da- ido kan ambaliyar da ta rutsa da dubban mutane a garin.

Shattima ya tabbatar wa ‘yan Najeriya cewa gwamnatin shugaba Bola Ahmed Tinubu za ta sa kafar wando-daya da kalubalen ambaliyar ruwa a kasar ta hanyar amfani da taswirar da za ta kawo maslaha ta dindindin.

Shettima, wanda ke jawabin cikin kaduwa a lokacin da yake tantance irin barnar da ambaliyar ta yi a garin Maiduguri, ya jajanta wa wadanda ibtila’in ya rutsa da su, inda ya bayyana musu cewa, shugaba Tinubu na tare da al’ummar da abin ya shafa, kuma gwamnatin tarayya za ta samar da dukkan abinda ake bukata domin tabbatar da tsaro da tallafawa mutanen da lamarin ya shafa.

Shettima ya danganta ambaliyar da ballewar madatsar ruwa ta Alau wanda ya ta’azzara lamarin har ya zarce irin wanda aka taba samu a baya. Sai dai kuma ya jaddada aniyarsa ta samar da mafita mai dorewa.

haka kuma ya yi kira da a ci gaba da wayar da kan al’umma kan karuwar barazanar da sauyin yanayi ke haifarwa tare da jaddada aniyar gwamnati ta magance wadannan kalubalen gaba daya.

Shettima, ya kuma yaba wa gwamnati da al’ummar jihar Borno bisa namijin kokarin da suka nuna wajen daukar matakan da suka dace akan lokaci tare da kai dauki ga al’ummar da lamarin ya shafa a cikin gaugawa.

PRNigeria Hausa

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp