Home General Adadin mutanen da ambaliya ta kashe a Maiduguri ya kai 30- NEMA

Adadin mutanen da ambaliya ta kashe a Maiduguri ya kai 30- NEMA

Hukumar bayar da agajin gaggawa a Najeriya NEMA ta fara tattara alƙaluman mutanen da suka rasa rayukansu  bayana aukuwar  ibtila’in ambaliyar ruwan a birnin Maiduguri na jihar Borno dake arewa maso gabashin Nijeriya a cikin daren Talatar da ta gabata.

Mahukuntan jihar sun ce zuwa yanzu an tattara gawarwakin mutane 30 yayin da NEMA ke ci gaba da aikin laluben waɗanda suka maƙale a saman rufin gidaje da wurare masu haɗari.

Hukumar NEMA ta ce ambaliyar ta shafi mutane miliyan 1 da rabi waɗanda ke halin tsananin buƙatar agaji, musamman ganin yadda suka bar muhallansu a yanayi na ɗimuwa sakamakon mummunar ambaliyar wadda ta faro da tsakaddaren Talata.

Kakakin hukumar ta NEMA Ezekiel Manzo ya shaidawa kamfanin dillancin labarai na AFP cewa kawo yanzu mutane 30 suka tabbatar da mutuwarsu ko da ya ke alƙaluman ka iya ƙaruwa sakamakon yadda har yanzu aka gaza gano mutane da dama da suka bace a ruwan.

Tun farko ɓallewar madatsar ruwa ta Alau ita ta haddasa tumbatsar ruwa a tituna da magudanan Maiduguri wanda zuwa yanzu ya lalata tarin kadarorin da ba a kai ga ƙiyasin ƙudinsu ba, baya ga ginaku da gidajen jama’a da kuma wuraren kasuwanci.

PRNigeria hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp