Home General Mutum 67 ne suka kamu da kyandar biri a Nijeriya – NCDC

Mutum 67 ne suka kamu da kyandar biri a Nijeriya – NCDC

Gwamnatin Nijeriya ta tabbatar da mutum 67 ne suka kamu da cutar kyandar biri daga cikin mutum 1,031 da aka yi fargabar sun kamu da cutar a jihohi 23, ciki har da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Hukumar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa, NCDC ce ta bayyana hakan inda ta ce jihohin Akwa-Ibom da Enugu kowacce na da mutum takwas da suka kamu, sai Bayelsa da ke da shida, sai kuma Cross-River mai biyar, da kuma sauran mutum 40 ɗin da suka watsu a sauran jihohi 19.

Darakta Janar na NCDC, Jide Idris ya ce hukumar ta ƙara zage damtse domin yaƙi da yaɗuwar cutar.

“Muna aiki tare da hukumomin tashashin jiragen ruwa domin kiyaye yiwuwar shigo mana da nau’in Clade I na cutar,” inji Idris, inda ya ƙara da cewa suma hukumomin na tashashin jiragen ruwa suna tattaunawa da jihohin da suke bakin boda.

Ya kuma ce suna ƙara inganta ɗakunan gwaje-gwajensu a faɗin ƙasar domin tabbatar da cewa ba sai an yi ta yin jigila ba domin gwajin cutar.

Zuwa yanzu dai ƙasashe 13 ne suka fama da cutar kyandar biri a Afirka bayan ƙasar Guinea ta sanar da mutum na farko da ya kamu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp