Home General Mutum 67 ne suka kamu da kyandar biri a Nijeriya – NCDC

Mutum 67 ne suka kamu da kyandar biri a Nijeriya – NCDC

Gwamnatin Nijeriya ta tabbatar da mutum 67 ne suka kamu da cutar kyandar biri daga cikin mutum 1,031 da aka yi fargabar sun kamu da cutar a jihohi 23, ciki har da Babban Birnin Tarayya Abuja.

Hukumar Yaƙi da Cututtuka Masu Yaɗuwa, NCDC ce ta bayyana hakan inda ta ce jihohin Akwa-Ibom da Enugu kowacce na da mutum takwas da suka kamu, sai Bayelsa da ke da shida, sai kuma Cross-River mai biyar, da kuma sauran mutum 40 ɗin da suka watsu a sauran jihohi 19.

Darakta Janar na NCDC, Jide Idris ya ce hukumar ta ƙara zage damtse domin yaƙi da yaɗuwar cutar.

“Muna aiki tare da hukumomin tashashin jiragen ruwa domin kiyaye yiwuwar shigo mana da nau’in Clade I na cutar,” inji Idris, inda ya ƙara da cewa suma hukumomin na tashashin jiragen ruwa suna tattaunawa da jihohin da suke bakin boda.

Ya kuma ce suna ƙara inganta ɗakunan gwaje-gwajensu a faɗin ƙasar domin tabbatar da cewa ba sai an yi ta yin jigila ba domin gwajin cutar.

Zuwa yanzu dai ƙasashe 13 ne suka fama da cutar kyandar biri a Afirka bayan ƙasar Guinea ta sanar da mutum na farko da ya kamu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp