Home General Gwamnatin Kano ta dakatar da tsawaita wa’adin ma’aikata 4,000 da Ganduje ya...

Gwamnatin Kano ta dakatar da tsawaita wa’adin ma’aikata 4,000 da Ganduje ya yi

Aƙalla ma’aikan jihar Kano 4,000 da gwamnatin tsohon gwamnan Abdullahi Umar Ganduje ta tsawaita wa wa’adin aiki ne ake sa ran za su ritaya a ranar 1 ga Disamban 2024.

Gwamnatin jihar ta ce ta kammala bincike da tantace ma’aikatan, waɗanda aka yi wa ƙarin wa’adin aiki bayan sun kai shekara 35 suna aiki, ko kuma sun kai shekara 60 a duniya.

Ganduje ne ya assasa shirin tsawaita wa’adin aiki a jihar, inda ma’aikata za su iya cigaba da aiki har na tsawon shekara biyar bayan sun kai lokacin ritaya.

Bayan gwamna Abba Yusuf ya ɗare karagar mulki a ranar 29 ga Mayun 2023 ne ya soke wannan ƙudurin, sannan ya yi umarni a dawo da shekarun ritayar shekara 35 ana aiki ko kuma shekara 60 a rayuwa.

Da yake zantawa da manema labarai, Shugaban Ma’aikatan jihar, Abdullahi Musa ya ce bayan an soke ƙudurin ne, aka kafa kwamiti domin kididdige adadin ma’aikatan.

“Bayan bincike ne kwamitinmu ya gano cewa kusan ma’aikata 4,000 suke cikin wannan tsarin, amma za su yi ritaya a 1 ga Disamban 2024. Wannan na nufin a ƙarshen watan Satumba za su miƙa takardar ajiye aiki,” inji shi kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Sai dai Abdullahi Musa ya ƙara da cewa gwamnati ta shirye maye gurbin da za su bari bayan sun yi ritayar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp