Home General Gwamnatin kano ta bayyana ranar komawa makarantu a jihar

Gwamnatin kano ta bayyana ranar komawa makarantu a jihar

Gwamnatin Jihar Kano ta saka ranar 16 ga watan Satumba domin komawa makarantar Firamare da Sakandire na zangon farko na shekarar 2024/2025 ga dukkan makarantun kwana da na firamare masu zaman kansu dake jihar.

Wannan na cikin wata sanarwa da Daraktan wayar da kan jama’a na ma’aikatar ilimi ta jihar, Balarabe Abdullahi Kiru ya sanya wa hannu aka raba ta ga manema labarai a jihar, wadda ta ce ta iyaye da wakilansu su lura da sabuwar ranar da za su ci gaba da aiki domin tabbatar da bin doka.

sanarwar ta ce Makarantun kwana a fadin jihar za su koma ranar Litinin 16 ga Satumba, 2024.

Idan dai ba a manta ba, kwamishinan ilimi na jihar Alhaji Umar Haruna Doguwa ya sanar a ranar Asabar 7 ga watan Satumba, dage ranar da za a koma makaranta.

Sanarwar ta sake jaddada kudurin gwamnatin Alhaji Abba Kabir Yusif na ganin kowane yaro ya samu ilimi mai inganci.

“Gwamnati na daukar matakai masu kyau wajen samar da ingantaccen yanayin koyo da zai zaburarwa da karfafawa dalibanmu kwarin gwiwa a fannin ilimi,” in ji sanarwar.

PRNigeria Hausa

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp