Home General Kotu ta ba da belin masu zanga-zangar tsadar rayuwa kan miliyan 10

Kotu ta ba da belin masu zanga-zangar tsadar rayuwa kan miliyan 10

Wata kotu a Abuja babban birnin Najeriya ta bayar da belin mutum 10 da ake tuhuma da cin amanar ƙasa yayin zanga-zanga kan tsadar rayuwa.

Mai Shari’a Emeka Nwite ya ce ya ba da belin maza tara da mace ɗaya, waɗanda ba su amsa tuhumar da ake yi musu ba kan naira miliyan 10 kowannensu.

Cikin tuhume-tuhumen da ake yi musu har da haɗa baki wajen tunzira sojoji su kifar da gwamnatin Bola Tinubu a zanga-zangar da suka gudanar a watan Agusta.

Sai dai tun da farko masu shigar da ƙara sun nemi kotun ta yi watsi da neman belin a makon da ya gabata.

Waɗanda ake zargin na iya fuskantar hukuncin kisa idan aka kama su da aikata laifukan da ake tuhumar su.

Alƙalin ya ɗage cigaba da sauraron ƙarar har zuwa ranar 27 ga watan Satumba. Sai dai ƙungiyar kare haƙƙi ta Amnesty International ta nemi gwamnati ta sake su ba tare da wani sharaɗi ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp