Home General Sojojin Najeriya sun kama masu safarar bindigogi biyar a Filato

Sojojin Najeriya sun kama masu safarar bindigogi biyar a Filato

Dakarun sojin Najeriya sun ce sun kama mutum biyar waɗanda suka shahara wajen safarar bindigogi a jihar Filato tare kuma da ƙwato makamai.

Wata sanarwa da jami’in yaɗa labarai na sojojin Manjo Stephen Zhakom ya fitar ranar Talata, ya ce an samu nasarar ce bayan wani aikin samame da suka kai jihar, inda ya ce hakan na cikin zimmar sojoji na ganin sun kakkaɓe masu rike da makamai ba bisa ka’ida ba.

“An fara samamen da dakarun Operation Safe Haven suka yi tare da haɗin gwiwar wasu jami’an tsaro ne a ranar Litinin da daddare har zuwa safiyar yau Talata,” in ji shi.

Ya ce dakarun sun yi wa maɓoyar wani mai safarar bindigogi mai suna Mohammed Sani a garin Naraguta kan hanyar Bauchi zuwa Jos, inda nan ne kuma suka yi nasarar kama shi tare da wasu mutum huɗu.

Makamai da sojojin suka kwace sun haɗa da bindigar AK-47 guda biyu, alburusai da sauransu.

Zhakom ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan mutanen da aka kama d anufin ƙara samun bayanai da za su kai ga kama sauran masu harkar domin daƙile aikinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp