Home AFIRKA Sojojin Mali sun ce sun magance harin da aka kai Bamako

Sojojin Mali sun ce sun magance harin da aka kai Bamako

Gwamnatin mulkin sojin Mali ta ce ta yi nasarar daƙile wani harin ta’addanci a babban birnin ƙasar, tana mai cewa yanzu hankula sun kwanta.

Rundunar sojin ƙasar tana gudanar da aikin tabbatar da tsaro bayan fafatawar da ta yi da ƴan bindigar da suka ƙaddamar da farmaki kan wata Cibiyar Ƴan sanda a Bamako.

A sanyin safiyar wannan Talatar ce, ƴan bindigar suka kai farmakin a kusa da filin jiragen sama kamar yadda wasu da suka shaida lamarin suka bayyana, inda suka tabbatar cewa, lallai sun ji ƙarar harbe-harbe da fashe-fashen bama-bamai.

Kamfanin Dillancin Labarai na AFP ya rawaito cewa, an kulle filin jiragen saman na wani  ɗan lokaci sakamakon fargabar abin da ka iya faruwa.

Tuni rundunar sojin ƙasar ta buƙaci mazauna yankin da su yi ƙaura na wucen-gadi kafin fitar da wata sabuwar sanarwa nan gaba.

Tun bayan juyin mulkin 2021, gwamnatin mulkin sojin Mali ke yaƙi da ƙungiyoyin ƴan ta’adda da suka haɗa da ƴan aware da mayaƙan jihadi masu alaka da al-Qaeda da ISIL.

A ƙarƙashin jagorancin shugaban mulkin sojin Mali, Kanar Assimi Goita, ƙasar ta yanke hulɗa da aminanta na ƙasashen Turai da kuma tsohuwar uwargijiyarta, Faransa, inda ta karkata hankalinta kan kulla alaƙa da Rasha da sojojin haya na Wagner domin samun agaji a fannin yaƙi da ƴan ta’adda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp