Home AFIRKA Sojojin Mali sun ce sun magance harin da aka kai Bamako

Sojojin Mali sun ce sun magance harin da aka kai Bamako

Gwamnatin mulkin sojin Mali ta ce ta yi nasarar daƙile wani harin ta’addanci a babban birnin ƙasar, tana mai cewa yanzu hankula sun kwanta.

Rundunar sojin ƙasar tana gudanar da aikin tabbatar da tsaro bayan fafatawar da ta yi da ƴan bindigar da suka ƙaddamar da farmaki kan wata Cibiyar Ƴan sanda a Bamako.

A sanyin safiyar wannan Talatar ce, ƴan bindigar suka kai farmakin a kusa da filin jiragen sama kamar yadda wasu da suka shaida lamarin suka bayyana, inda suka tabbatar cewa, lallai sun ji ƙarar harbe-harbe da fashe-fashen bama-bamai.

Kamfanin Dillancin Labarai na AFP ya rawaito cewa, an kulle filin jiragen saman na wani  ɗan lokaci sakamakon fargabar abin da ka iya faruwa.

Tuni rundunar sojin ƙasar ta buƙaci mazauna yankin da su yi ƙaura na wucen-gadi kafin fitar da wata sabuwar sanarwa nan gaba.

Tun bayan juyin mulkin 2021, gwamnatin mulkin sojin Mali ke yaƙi da ƙungiyoyin ƴan ta’adda da suka haɗa da ƴan aware da mayaƙan jihadi masu alaka da al-Qaeda da ISIL.

A ƙarƙashin jagorancin shugaban mulkin sojin Mali, Kanar Assimi Goita, ƙasar ta yanke hulɗa da aminanta na ƙasashen Turai da kuma tsohuwar uwargijiyarta, Faransa, inda ta karkata hankalinta kan kulla alaƙa da Rasha da sojojin haya na Wagner domin samun agaji a fannin yaƙi da ƴan ta’adda.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp