Home General Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Zabe Edo- IG ya bayar da umarnin takaita zirga-zirga a jihar

Babban sifeton ‘yansandan Najeriya, Kayode Egbetokun ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirga a jihar Edo a lokacin zaɓen gwamnan jihar da za a gudanar ranar Asabar.

Cikin wata sanarwa da jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yansandan ƙasar, Olumiyiwa Adejobi ya fitar, babban sifeton ya bayar da umarnin taƙaita zirga-zirgar ababen hawa a kan tituna da ruwa da sauran hanyoyin sufuri tun daga ƙarfe 6:00 na safe zuwa 6:00 na maraice a ranar zaɓen.

To sai dai sanarwar ta iyakance masu muhimman ayyuka, ciki har da ‘yan jaridar da aka tantance da jami’an zaɓe da motocin ɗaukar marasa lafiya da masu kai ɗaukin gaggawa.

”Domin tabbatar da sahihancin zaɓen, babban sifeton ‘yansandan ya haramta wa duka jami’an tsaron da ke tsare ko raka manyan mutane zuwa rumfunan zaɓe ko cibiyoyin tattara sakamakon zaɓen”, kamar yadda sanarwar ta yi ƙarin haske.

Haka kuma sanarwar ta haramta aikin jami’an tsaron sa kai a faɗin jihar a lokacin zaɓen, haka kuma an haramta jiniya ga ababen hawan da ba a amince wa ba, domin tabbatar da kwanciyar hankalin masu zaɓe.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp