Home General Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Tinubu ya taya Monday Okpebholo murnar lashe zaɓen gwamnan Edo

Shugaba Bola Tinubu ya taya zaɓaɓɓen gwamnan jihar Edo, Monday Okpebholo murnar lashe zaɓe.

Hukumar zaɓe mai zaman kanta ta INEC ce ta sanar da Okpebholo matsayin wanda ya lashe zaɓen da aka gudanar ranar Asabar 21 ga watan Satumba, inda ya doke sauran ƴan takara.

Wata sanarwa da mai bai wa shugaban shawara kan harkar yaɗa labarai Bayo Onanuga ya fitar a shafinsa na X, Tinubu ya yaba wa jagorancin jam’iyyar APC na ƙasa da kuma gwamnonin jam’iyyar bisa jajircewarsu wajen ganin an samu nasara.

Ya buƙaci sabon gwamnan jihar ta Edo da ya ɗauki nasarar a matsayin hakki da aka ɗora masa wajen kai jihar gaba.

“Nasarar ta nuna irin goyon baya da mutane ke yi wa jam’iyyar mu ta APC, ƙoƙari da take yi da kuma tsare-tsare da take ɓullo da su wajen inganta rayuwar ƴan Najeriya,” in ji Tinubu.

Ya ce Okpebholo ya nuna dattako wajen gayyato ƴan adawa domin a yi tafiya tare da kuma haɗa kan al’ummar jihar don samun ci gaba.

Shugaban Najeriyar ya kuma yaba yadda aka gudanar da zaɓen cikin kwanciyar hankali da lumana.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp