Home General Ambaliya: mutum 25 sun rasu, gidaje 312,000 sun rushe a Kebbi

Ambaliya: mutum 25 sun rasu, gidaje 312,000 sun rushe a Kebbi

Gwamnatin Kebbi ta ce aƙalla an yi asarar rayukan mutane 29 da gidaje 321,000 da gonaki 858,000 sanadiyyar ambaliyar ruwa a ƙananan hukumomi 16 daga cikin 21 na jihar.

Kwamishinan Labarai, Yakubu Ahmed Birnin Kebbi ne bayyana hakan a ranar Juma’a a yayin zantawa da manema labarai a cibiyar manema labarai da ke Birnin Kebbi.

Ya ce, idan ba ɗauki mataki a yankunan da abin ya shafa ba, wanda suka rasa shinkafa da Masara da dawa da sauran amfanin gona da ambaliyar ta lalata za a iya samun ƙarancin abinci a jihar da kasar.

Ya ce, kafin gargaɗin da Hukumar Hasashen Yanayi NIMET ta yi, jihar ta fuskanci ibtila’i mai tsanani sakamakon ambaliya a ƙananan hukumomi 16 na jihar a dalilin ruwan da aka sako daga Madatsar Ruwa ta Goronyo da kuma magudanar ruwa a kogin Rima da kogin kaa da ke kwararo tun daga Kogin Neja.

Kwamishinan ya ce duk da matakan da gwamnatin ta ɗauka har yanzu jihar na fama da ambaliyar ruwa a ƙananan hukumominta 16.

“Kananan hukumomi 5 daga cikin 21 na jihar ne kaɗai abin bai shafa ba. Ambaliyar ta lalata gonaki, gadoji da dubban gidaje.

“Game da adadin wadanda suka mutu, mun rasa mutane bakwai a Shanga, takwas a Maiyama, biyar a Kalgo. Kazalika, an rasa mutum bakwai a Jega, biyu kuma a Birnin Kebbi,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp