Home General Tinubu ya rantsar da Kudirat Kekere-Ekun babbar mai shari’a ta Najeriya

Tinubu ya rantsar da Kudirat Kekere-Ekun babbar mai shari’a ta Najeriya

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya rantsar da Mai Shari’a Kudirat Olatokunbo Kekere-Ekun domin kama aiki a matsayin babbar mai shari’a ta ƙasa a ranar Litinin bayan Majalisar Dattawa ta amince da naɗin nata.

Ita ce mace ta biyu da take riƙe muƙamin a tarihi, kamar yadda wata sanarwa daga fadar shugaban ƙasa ta bayyana.

An yi bikin rantsuwar ne a gaban tsofaffin manyan alƙalai huɗu, ciki har da mace ta farko da ta riƙe muƙamin Mariam Aloma Mukhtar.

“Fannin shari’a babban ginshiƙi ne da ke tallafe da tsarin dimokuɗaiyarmu, kuma tsawon shekaru fannin shari’ar Najeriya ya sha nuna tasirinsa na mai shiga tsakani domin tabbatar kowa ya bi doka,” a cewar Shugaba Tinubu yayin taron.

“Matsayinki na zama wuri na ƙarshe da talaka zai samu adalci yana da muhimmanci wajen saka wa mutane ƙwarin gwiwa kan dimokuraɗiyya,” in ji shi.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp