Home General Ku dai na Tsinewa Shuwagabannin- Sarkin Musulmi

Ku dai na Tsinewa Shuwagabannin- Sarkin Musulmi

Mai alfarma Sarkin Sokoto, Alhaji Sa’ad Abubakar III ya yi kira ga ƴan Najeriya da cewa da su riƙa yi wa shugabannin ƙasar addu’a duk yanayin da ake ciki, kuma duk yanayin da ƙasar ke ciki.

Sultan ya yi wannan kiran ne a Jami’ar Ilorin a ranar Alhamis a lokacin da yake gabatar da jawabi a taron ƙaddamar da littafin da aka rubuta a kan shugaban hukumar JAMB Farfesa Is’haq Oloyede, wanda ya yi ritaya daga aikin jami’a kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

Sultan ɗin ya ƙara cewa, “ku daina tsine wa shugabanni duk yadda abubuwa suka lalace, maimakon haka gara ku riƙa musu addu’a. Ku daina faɗin abubuwa marasa kyau a kansu. Duk lalacewar shugaba ku guji tsine masa,” in ji shi.

A nasa jawabin, ministan shari’a Lateef Fagbemi (SAN), wanda shi ne shugaban taron, kira ya yi ga ƴan Najeriya da su riƙa ƙarfafa wa shugabanninsu gwiwa.

“Ban ce babu matsala ba, amma da zarar kun fara ɓata ƙasarku a idon duniya, ban san me muke tuna wa duniya ba game da ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp