Home Labarai Akwai yiwuwar samun ambaliyar ruwa a a wasu jihohin Nijeriya 22

Akwai yiwuwar samun ambaliyar ruwa a a wasu jihohin Nijeriya 22

Gwamnatin Najeriya ta yi hasashen kwashe kwana biyar ana mamakon ruwa, wanda zai iya jawo ambaliya a jihohi 22 na babban birnin tarayyar ƙasar, inda ta yi gargaɗi ga garuruwan da suke bakin tekunan Donga da Binue da Ogun su tashi daga yankunan.

Jaridar Punch ce ta ruwaito hakan a ranar Litinin daga ma’aikatar muhalli.

Rohoton na kwamitin bayar da gargaɗi na ma’aikatar ya ƙara da cewa za a iya fuskantar ambaliyar ne a ranar 14 da 18 na watan Oktoba.

Jihohin da yankunan da za su iya fuskantar ambaliyar sun haɗa da jihar Osun (Ede, Ile-Ife, Ilesa, Osogbo); jihar Delta (Escravos); jihar Kuros Riba (Ikom); jihar Anambra (Onitsha); jihar Taraba (Donga, Ibi, Wukari, Bandawa, Beli, Bolleri, Dampar, Duchi, Garkowa, Gassol, Gungun Bodel, Kambari, Kwata Kanawa, Lau, Mayo Ranewo, Mutum Biyu, Ngaruwa, Serti, Yorro); jihar Nasarawa (Rukubi); jihar Kebbi (Argungu, Birnin-Kebbi, Gwandu, Kalgo, Ribah, Sakaba, Yelwa); jihar Gombe (Bajoga); jihar Katsina (Bakori, Funtua); jihar Borno (Biu, Briyel); jihar Kaduna (Birnin-Gwari, Buruku, Kaduna, Jaji); jihar Niger (Bida, Kontagora, Lapai, Lavun, Magama, Mashegu, Mokwa, New Bussa, Rijau, Sarkin Pawa, Suleja, Wushishi).

Sauran su ne jihar Yobe (Dapchi); Adamawa (Demsa, Farkumo, Ganye, Gbajili, Jimeta, Mayo-Belwa, Mubi, Natubi, Numan, Song, Shelleng, Wuro Bokki); Kogi (Ibaji, Omala); Kwara (Jebba, Kosubosu); Bauchi (Kari, Tafawa Balewa, Kirfi); Plateau (Shendam); babban birnin tarayya Abuja (Kubwa, Gwagwalada, Bwari); Kano (Sumaila); Oyo (Kishi); Sokoto (Silame); da Zamfara (Majara).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp