Home General Fashewar tankar mai ta kashe sama da mutum 100 a jihar Jigawa

Fashewar tankar mai ta kashe sama da mutum 100 a jihar Jigawa

Wata tanka ɗauke da man fetur ta yi sanadiyyar kashe sama da mutum 100 a jihar Jigawa da ke arewacin Najeriya bayan ta faɗi tare da kamawa da wuta.

Babbar jami’ar hukumar kiyaye haɗurra a Jigawa, Aishatu Sa’adu, ta ce zuwa yanzu mutum 104 ne suka mutu sakamakon hatsarin da ya faru ranar Talata da dare.

Da take magana yayin da ta isa wurin da lamarin ya faru a garin Majiya na ƙaramar hukumar Taura, Aisha ta ce wasu mutum 100 sun jikkata.

Tun da farko ta ce ibtila’in ya faru ne bayan da direban tankar ya kauce wa wata babbar mota ɗauke da tumatur.

Hakan ya sa direban tankar ya faɗa gefen titin har kan motar ya rabu da gangar jikinta, lamarin da ya sa fetur ɗin da yake dako ya malale titi da kwatoci a gefen hanyar.

Kakakin rundunar ‘yansanda a Jigawa, DSP Lawan Adam, ya ce ganin haka ne ya sa mutane suka yi dafifi a wurin da lamarin ya faru domin kwasar man da ya zuba a ƙasa bayan sun ci ƙarfin jami’an tsaron da ke korarsu a ƙokarin kauce wa tashin gobara.

Shaidu sun shaida wa BBC cewa tankar ta yi kusan awa biyu tana ci da wuta kafin jami’an kashe gobara su yi nasarar kashe ta.

Zuwa yanzu ana shirin yin jana’izar mutanen da suka mutu sakamakon fashewar tankar.

Hotunan da aka turo wa BBC sun nuna yadda aka lulluɓe gawarwakin mutanen da ganyayyaki, yayin da wasu hotunan suke ɗauke da gawarwakin da suka rasa wasu sassa na jikinsu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp