Home Labarai NASSI Da BOI Sun Sanya Hannu Akan Yarjejeniyar Bawa Ƙananan Masana’antu Rancen...

NASSI Da BOI Sun Sanya Hannu Akan Yarjejeniyar Bawa Ƙananan Masana’antu Rancen Bilyan 75

Ƙungiyar masu ƙanana da matsakaitan Masana’antu ta Najeriya, wato Nigeria Association of Small Scale Industrialists (NASSI), ta sanya hannu akan wata yarjejeniya da Bankin Masana’antu wato Bank of Industry, wadda ta sahale a bawa Mambobin ƙungiyar rancen naira Bilyan 75.

Shugaban NASSI na ƙasa Chief Dakta Solomon Daniel Vonfa ne ya sanya hannu akan takardar yarjejeniya, a inda shi kuma Manajan Daraktan Bankin Dakta Olasupo Olusi ya sanya hannu domin fara aiwatar da wannan tsari.

Da yake yiwa jaridar PRNigeria ƙarin haske, Babban Ma’ajin Ƙungiyar NASSI na ƙasa, Dakta Abubakar Tanko Bala ya ce manufar shirin shine nema wa Mambobinta rancen da zasu inganta kasuwancin su.

Ya kuma ƙara da cewa an kasa tsarin gida Uku, ta yadda kashin farko za’a bawa masu manyan Masana’antu rancen naira Bilyan 75, sai ɓangaren su na masu ƙananan da matsakaitan Masana’antu inda suma zasu amfana da naira Bilyan 75, da kuma masu sana’oi na gida (Nano Program) su kuma zasu amfana da Naira Bilyan 50.

Bugu da ƙari ƙungiyar ta bayyana matuƙar farin cikin ta, a bisa yadda Bankin ya basu tabbacin cewa sune zasu fitar da Jadawalin waɗanda zasu amfana da wannan tsari na Rancen naira Bilyan 75 ga ƙananan da matsakaitan Masana’antun dake faɗin ƙasar.

Haka kuma yarjejeniyar ta ƙunshi yadda za’a wayar da kan masu ƙananan Masana’antu dama basu bitar yadda zasu inganta kasuwancin su ko kuma Kamfanoni dake faɗin ƙasar.

A cewar Dakta Tanko, “Wannan shiri na cikin Kyawawan ƙudirrikan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na nemawa talakawan ƙasar mafita a sakamakon irin halin da aka tsinci kai a ciki na matsi da taɓarɓarewar tattalin arziƙi”.

domin haka ne ƙungiyar ta buƙaci dukkan Mambobin ta dake Jihohin Najeriya 36 da babban birnin tarayya Abuja su yi gaggawar shiga wannan tsari domin ya zamana sun ci gajiyar shirin ta yadda zasu bunƙasa harkokin kasuwancin nasu dama tattallin arziƙin ƙasar.

A ƙarshe Babban Ma’ajin ƙungiyar yayi fatan dukkan waɗanda suka sami wannan rance zasu yi amfani dashi ta hanyar da ta dace, kuma su dawo dashi cikin wannan lokaci da aka ƙayyade.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp