Home Labarai NASSI Da BOI Sun Sanya Hannu Akan Yarjejeniyar Bawa Ƙananan Masana’antu Rancen...

NASSI Da BOI Sun Sanya Hannu Akan Yarjejeniyar Bawa Ƙananan Masana’antu Rancen Bilyan 75

Ƙungiyar masu ƙanana da matsakaitan Masana’antu ta Najeriya, wato Nigeria Association of Small Scale Industrialists (NASSI), ta sanya hannu akan wata yarjejeniya da Bankin Masana’antu wato Bank of Industry, wadda ta sahale a bawa Mambobin ƙungiyar rancen naira Bilyan 75.

Shugaban NASSI na ƙasa Chief Dakta Solomon Daniel Vonfa ne ya sanya hannu akan takardar yarjejeniya, a inda shi kuma Manajan Daraktan Bankin Dakta Olasupo Olusi ya sanya hannu domin fara aiwatar da wannan tsari.

Da yake yiwa jaridar PRNigeria ƙarin haske, Babban Ma’ajin Ƙungiyar NASSI na ƙasa, Dakta Abubakar Tanko Bala ya ce manufar shirin shine nema wa Mambobinta rancen da zasu inganta kasuwancin su.

Ya kuma ƙara da cewa an kasa tsarin gida Uku, ta yadda kashin farko za’a bawa masu manyan Masana’antu rancen naira Bilyan 75, sai ɓangaren su na masu ƙananan da matsakaitan Masana’antu inda suma zasu amfana da naira Bilyan 75, da kuma masu sana’oi na gida (Nano Program) su kuma zasu amfana da Naira Bilyan 50.

Bugu da ƙari ƙungiyar ta bayyana matuƙar farin cikin ta, a bisa yadda Bankin ya basu tabbacin cewa sune zasu fitar da Jadawalin waɗanda zasu amfana da wannan tsari na Rancen naira Bilyan 75 ga ƙananan da matsakaitan Masana’antun dake faɗin ƙasar.

Haka kuma yarjejeniyar ta ƙunshi yadda za’a wayar da kan masu ƙananan Masana’antu dama basu bitar yadda zasu inganta kasuwancin su ko kuma Kamfanoni dake faɗin ƙasar.

A cewar Dakta Tanko, “Wannan shiri na cikin Kyawawan ƙudirrikan Shugaban Ƙasa Bola Ahmed Tinubu, na nemawa talakawan ƙasar mafita a sakamakon irin halin da aka tsinci kai a ciki na matsi da taɓarɓarewar tattalin arziƙi”.

domin haka ne ƙungiyar ta buƙaci dukkan Mambobin ta dake Jihohin Najeriya 36 da babban birnin tarayya Abuja su yi gaggawar shiga wannan tsari domin ya zamana sun ci gajiyar shirin ta yadda zasu bunƙasa harkokin kasuwancin nasu dama tattallin arziƙin ƙasar.

A ƙarshe Babban Ma’ajin ƙungiyar yayi fatan dukkan waɗanda suka sami wannan rance zasu yi amfani dashi ta hanyar da ta dace, kuma su dawo dashi cikin wannan lokaci da aka ƙayyade.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp