Home General Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Wasu da ake zargin ƴan bimdiga sun kashe mutum biyar a wani sabon hari da suka kai karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang shi ya tabbaatr da faruwar hakan a jiya Talata.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa irin harin ya janyo mutuwar mutane biyar bayan kwantan-ɓauna da ƴan bindigar suka yi musu.

“Harin ya yi sanadiyyar rayukan matasa huɗu waɗanda suka fito domin tsare gidajensu. Bayan nan maharan sun kuma kashe wani tsoho bayan yin dirar miƙiya zuwa cikin gidansa,” in ji Fuddang.

Harin dai na zuwa ne ƙasa da mako ɗaya da kai wasu hare-hare, inda aka kashe wasu mutane goma a karamar hukumar ta hanyar yi musu kisan gilla.

Al’ummar yankin sun yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarinsu na fatattakar ƴan bindigar, inda suka yi kira na a ƙara kaimi tare da haɗin gwiwa wajen daƙile irin waɗannan hare-hare a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp