Home General Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Ƴan bindiga sun kashe mutum biyar a wani hari a Filato

Wasu da ake zargin ƴan bimdiga sun kashe mutum biyar a wani sabon hari da suka kai karamar hukumar Bokkos na jihar Filato.

Shugaban ƙungiyar ci gaban al’ummar Bokkos, Farmasum Fuddang shi ya tabbaatr da faruwar hakan a jiya Talata.

Ya shaida wa gidan talabijin na Channels cewa irin harin ya janyo mutuwar mutane biyar bayan kwantan-ɓauna da ƴan bindigar suka yi musu.

“Harin ya yi sanadiyyar rayukan matasa huɗu waɗanda suka fito domin tsare gidajensu. Bayan nan maharan sun kuma kashe wani tsoho bayan yin dirar miƙiya zuwa cikin gidansa,” in ji Fuddang.

Harin dai na zuwa ne ƙasa da mako ɗaya da kai wasu hare-hare, inda aka kashe wasu mutane goma a karamar hukumar ta hanyar yi musu kisan gilla.

Al’ummar yankin sun yaba wa jami’an tsaro bisa ƙoƙarinsu na fatattakar ƴan bindigar, inda suka yi kira na a ƙara kaimi tare da haɗin gwiwa wajen daƙile irin waɗannan hare-hare a yankin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp