Home AFIRKA Kotu tayi watsi da bukatar mataimakin shugaban Kenya kan yunkurin tsige shi

Kotu tayi watsi da bukatar mataimakin shugaban Kenya kan yunkurin tsige shi

Kotu a Kenya ta yi watsi da buƙatar da mataimakin shugaban ƙasar Rigathi Gachagua ya gabatar, inda yake nema a hana Majalisar Dattawan gudanar da mahawara da kuma kaɗa  kuri’a domin tsige shi.

Lokacin da yake yanke wannan hukunci a jiya talata, alƙalin babbar kotun mai shari’a Enock Chacha Mwita, ya ce ta la’akari da abubuwan da ke ƙunsh a kundin tsarin mulki, majalisar dokoki tana da damar gudanar da bincike kan duk wani zargi da ake yi wa mataimakin shugaban ƙasa, saboda haka yunƙuri domin hana wannan bincike zai kasance iya kasancewa karen-tsaye ga dokokin ƙasar.

To sai dai duk da cewa bai kasance a cikin zauren shari’ar ba, amma lauyen da ke kare mataimakin shugaban ƙasar ya ce za su ɗaukaka don nuna rashin gamsuwa a game da wannan hukunci.

Tun a cikin makon jiya ne ƙaramar majalisar dokokin Kenya ta kaɗa ƙuri’ar tsige Mista Gachagua mai shekaru 59 a duniya, saboda a cewarta ta same shi da laifin ƙin yi wa shugaban ƙasa William Ruto biyayya sannan kuma ya handame dukiyar al’umma.

Kamar dai yadda yake rubuce a cikin kundin tsarin mulki, ana buƙatar ƙuri’u 45 daga cikin 68 da ake da su a cikin majalisar dattawa ne domin tsige mataimakin shugaban, kuma idan hakan ya tabbata, Rigathi Gachagua zai kasance mataimakin shugaban ƙasar Kenya na farko da aka tuɓe daga mukaminsa a tarihin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp