Home AFIRKA Kotu tayi watsi da bukatar mataimakin shugaban Kenya kan yunkurin tsige shi

Kotu tayi watsi da bukatar mataimakin shugaban Kenya kan yunkurin tsige shi

Kotu a Kenya ta yi watsi da buƙatar da mataimakin shugaban ƙasar Rigathi Gachagua ya gabatar, inda yake nema a hana Majalisar Dattawan gudanar da mahawara da kuma kaɗa  kuri’a domin tsige shi.

Lokacin da yake yanke wannan hukunci a jiya talata, alƙalin babbar kotun mai shari’a Enock Chacha Mwita, ya ce ta la’akari da abubuwan da ke ƙunsh a kundin tsarin mulki, majalisar dokoki tana da damar gudanar da bincike kan duk wani zargi da ake yi wa mataimakin shugaban ƙasa, saboda haka yunƙuri domin hana wannan bincike zai kasance iya kasancewa karen-tsaye ga dokokin ƙasar.

To sai dai duk da cewa bai kasance a cikin zauren shari’ar ba, amma lauyen da ke kare mataimakin shugaban ƙasar ya ce za su ɗaukaka don nuna rashin gamsuwa a game da wannan hukunci.

Tun a cikin makon jiya ne ƙaramar majalisar dokokin Kenya ta kaɗa ƙuri’ar tsige Mista Gachagua mai shekaru 59 a duniya, saboda a cewarta ta same shi da laifin ƙin yi wa shugaban ƙasa William Ruto biyayya sannan kuma ya handame dukiyar al’umma.

Kamar dai yadda yake rubuce a cikin kundin tsarin mulki, ana buƙatar ƙuri’u 45 daga cikin 68 da ake da su a cikin majalisar dattawa ne domin tsige mataimakin shugaban, kuma idan hakan ya tabbata, Rigathi Gachagua zai kasance mataimakin shugaban ƙasar Kenya na farko da aka tuɓe daga mukaminsa a tarihin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp