Home AFIRKA Kotu tayi watsi da bukatar mataimakin shugaban Kenya kan yunkurin tsige shi

Kotu tayi watsi da bukatar mataimakin shugaban Kenya kan yunkurin tsige shi

Kotu a Kenya ta yi watsi da buƙatar da mataimakin shugaban ƙasar Rigathi Gachagua ya gabatar, inda yake nema a hana Majalisar Dattawan gudanar da mahawara da kuma kaɗa  kuri’a domin tsige shi.

Lokacin da yake yanke wannan hukunci a jiya talata, alƙalin babbar kotun mai shari’a Enock Chacha Mwita, ya ce ta la’akari da abubuwan da ke ƙunsh a kundin tsarin mulki, majalisar dokoki tana da damar gudanar da bincike kan duk wani zargi da ake yi wa mataimakin shugaban ƙasa, saboda haka yunƙuri domin hana wannan bincike zai kasance iya kasancewa karen-tsaye ga dokokin ƙasar.

To sai dai duk da cewa bai kasance a cikin zauren shari’ar ba, amma lauyen da ke kare mataimakin shugaban ƙasar ya ce za su ɗaukaka don nuna rashin gamsuwa a game da wannan hukunci.

Tun a cikin makon jiya ne ƙaramar majalisar dokokin Kenya ta kaɗa ƙuri’ar tsige Mista Gachagua mai shekaru 59 a duniya, saboda a cewarta ta same shi da laifin ƙin yi wa shugaban ƙasa William Ruto biyayya sannan kuma ya handame dukiyar al’umma.

Kamar dai yadda yake rubuce a cikin kundin tsarin mulki, ana buƙatar ƙuri’u 45 daga cikin 68 da ake da su a cikin majalisar dattawa ne domin tsige mataimakin shugaban, kuma idan hakan ya tabbata, Rigathi Gachagua zai kasance mataimakin shugaban ƙasar Kenya na farko da aka tuɓe daga mukaminsa a tarihin ƙasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp