Home General An samu karuwar masu fama da matsalar tamowa a Najeriya – ICRC

An samu karuwar masu fama da matsalar tamowa a Najeriya – ICRC

Kungiyar agaji ta duniya ICRC ta ce an samu karuwar matsalar tamowa a yankin arewa maso gabashin Najeriya abinda ya kai ga cikar asibitoci da cibiyoyin kula da lafiyar yankin da marasa lafiya.

Rahotan da kungiyar ICRC ta fitar ya ce cibiyoyin kula da lafiyar sun sanar da samun karuwar akalla kashi 24 na yawan yaran dake fama da karancin abinci mai gina jiki sabanin adadin da aka gani a shekarar da ta gabata.

Hukumar na danganta wannan matsalar da matsalolin da suka addabi yankin irin na tashe tashen hankula da kuma farin da ya hana mutane samun abinci mai gina jiki da za su ciyar da yaran su.

Wata mata da ake kira Rabiatu Jibrilla ta ce lokacin da ta kai yaron ta cibiyar kula da lafiyar ko zama baya iya yi, yayin da cikin sa ya shanye kamar babu hanji a ciki.

ICRC ta ce a watanni 3 na biyun wannan shekara ta yi rajistar karin yaran da suak kai kashi 48 da ke fama da tsananin rashin abinci mai gina jiki wadanda ke kasa da shekaru 5 a asibitocin da suke taimakawa sabanin abinda aka gani bara.

Kungiyar ta ce akalla yara miliyan 6 da dubu 100 a yankin Tafkin Chadi ke fuskantar barazanar karancin abinci mai gina jiki a watanni maus zuwa saboda ci gaba da tashin hankalin da ake fuskanta da kuma matsalar sauyin yanayi, adadi mafi girma da aka taba gani a cikin shekaru 4 da suka gabata.

ICRC ta ce tashin hankalin da ake fuskanta a yankin wanda ya sake ta’azzara a watanni 6 na farkon wannan shekarar shine dalilin fuskantar wannan yanayi mafi muni na karancin abinci, ganin yadda ya raba miliyoyin mutane da gidajen su da lalata hanyoyin sana’oin su tare da shafar noman da ake yi domin samun abinci.

Wani manomi da ake kira John Paul Ezra yace yanzu ba su da isassun filayen noma kamar yadda suke yi a shekarun baya saboda wannan matasalar ta tashe tashen hankula wadanda suka hana mutane zuwa gonakin dake nesa da gari a Madagali dake jihar Adamawa.

Shi kuwa Abubakar Bello Duhu dake kauyen Kwata Kwamla ya ce dogara da mutanen yankin suka yi da noman damina ya gamu da matsalar karancin ruwan sama wanda ya shafi abinda suke nomawa, ya yin da ambaliya kuma ke illa a wasu yankunan.

Kungiyar agaji ta ICRC na aiki tare da Red Cross a tsakanin al’ummar da ke yankin tare da  kananan hukumomi domin tallafa musu da kudaden da za su samar da irin dake jure fari da kuma maganin rigakafi na dabbobin su.

Shugaban tawagar ICRC a Mubi, Francesca Piccin ta ce suna kokarin inganat taimakon da suke bai wa jama’ar yankin, sai dai bukatun jama’ar ya zarce abinda suke ba su.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp