Home Labarai Gwamnan Kano ya karɓi rahoton mafi ƙarancin albashin ma’aikata

Gwamnan Kano ya karɓi rahoton mafi ƙarancin albashin ma’aikata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin ma’aikatan gwamnati yayin da ya karɓi rahoton da aka jima ana jira daga kwamitin mafi karancin albashi na jihar.

Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar aka raba manema labarai a jihar Kano a ranar Talata.

Kwamitin, ƙarƙashin jagorancin Usman Bala, mai baiwa Gwamna shawara kan al’amuran jiha, an ɗora masa nauyin duba da kuma bada shawarar inganta tsarin albashi mafi ƙankanta na jihar.

Yayin miƙa rahoton, Gwamna Yusuf ya nuna gamsuwarsa sosai da aikin kwamitin, inda ya yaba musu bisa cikakken bincike da tuntuɓar da suka gudanar.

Ya jaddada cewa shawarwarin kwamitin za su taimaka wa gwamnati wajen aiwatar da manufofi da suka dace da tsarin tattalin arzikin jihar kuma masu ɗorewa.

“Mun zaɓi wannan kwamiti ne saboda muna da imani da ƙarfin basirarsu wajen ba da shawarwari masu fa’ida da sabbin dabaru don ci gaba,” inji gwamnan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp