Home Labarai Rushe shugabancin KANSIEC ya haifar da cece-kuce a jihar Kano

Rushe shugabancin KANSIEC ya haifar da cece-kuce a jihar Kano

Majalisar jihar Kano
Majalisar jihar Kano

Majalisar dokokin jihar Kano ta tabbatar da cewa za a gudanar da zaben kananan hukumomi kamar yadda aka tsara a ranar Asabar 26 ga watan Oktoba, 2024, duk da hukuncin da babbar kotun tarayya ta yanke na hana hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano KANSIEC gudanar da zaben.

Wannan matsaya ta biyo bayan hukuncin da mai shari’a Simon Amobeda na babbar kotun tarayya da ke Kano ya yanke a ranar Talata,

Kotu tace wadanda aka bawa mukamin shugabannin hukumar basu cancanta saboda sun kasance magoya bayan jamiyyar NNPP mai mulkin Kano, dan haka kotun tace wadannan mutane basu da damar gudanar da zaben Ƙananan.
Sai dai gwamnatin jihar Kano ta bayyana kudirinta na ci gaba da gudanar da zaben, ko da kuwa hukumomin tsaro irin na ‘yan sanda ba sa iya ba da kariya.

Shugaban masu rinjaye na majalisar, Lawan Hussaini Dala, ya soki hukuncin kotun, yana mai cewa ya sabawa umarnin da mai shari’a Nura Ma’aji ya bayar a baya, wanda ya haramtawa jam’iyyun siyasa 19 ciki har da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) kalubalantar zabe.

“Hukuncin da kotun tarayya ta yanke na tsige shugaban KANSIEC ya ci karo da hukuncin da Mai shari’a Ma’aji ya yanke na hana jam’iyyun siyasa kutsawa cikin harkokin zabe,” in ji Dala.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp