Home Labarai Gwamnan Kano ya karɓi rahoton mafi ƙarancin albashin ma’aikata

Gwamnan Kano ya karɓi rahoton mafi ƙarancin albashin ma’aikata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin ma’aikatan gwamnati yayin da ya karɓi rahoton da aka jima ana jira daga kwamitin mafi karancin albashi na jihar.

Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar aka raba manema labarai a jihar Kano a ranar Talata.

Kwamitin, ƙarƙashin jagorancin Usman Bala, mai baiwa Gwamna shawara kan al’amuran jiha, an ɗora masa nauyin duba da kuma bada shawarar inganta tsarin albashi mafi ƙankanta na jihar.

Yayin miƙa rahoton, Gwamna Yusuf ya nuna gamsuwarsa sosai da aikin kwamitin, inda ya yaba musu bisa cikakken bincike da tuntuɓar da suka gudanar.

Ya jaddada cewa shawarwarin kwamitin za su taimaka wa gwamnati wajen aiwatar da manufofi da suka dace da tsarin tattalin arzikin jihar kuma masu ɗorewa.

“Mun zaɓi wannan kwamiti ne saboda muna da imani da ƙarfin basirarsu wajen ba da shawarwari masu fa’ida da sabbin dabaru don ci gaba,” inji gwamnan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp