Home Labarai Gwamnan Kano ya karɓi rahoton mafi ƙarancin albashin ma’aikata

Gwamnan Kano ya karɓi rahoton mafi ƙarancin albashin ma’aikata

Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf, ya sake jaddada kudirin gwamnatinsa na inganta jin daɗin ma’aikatan gwamnati yayin da ya karɓi rahoton da aka jima ana jira daga kwamitin mafi karancin albashi na jihar.

Bayanin hakan na ƙunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya fitar aka raba manema labarai a jihar Kano a ranar Talata.

Kwamitin, ƙarƙashin jagorancin Usman Bala, mai baiwa Gwamna shawara kan al’amuran jiha, an ɗora masa nauyin duba da kuma bada shawarar inganta tsarin albashi mafi ƙankanta na jihar.

Yayin miƙa rahoton, Gwamna Yusuf ya nuna gamsuwarsa sosai da aikin kwamitin, inda ya yaba musu bisa cikakken bincike da tuntuɓar da suka gudanar.

Ya jaddada cewa shawarwarin kwamitin za su taimaka wa gwamnati wajen aiwatar da manufofi da suka dace da tsarin tattalin arzikin jihar kuma masu ɗorewa.

“Mun zaɓi wannan kwamiti ne saboda muna da imani da ƙarfin basirarsu wajen ba da shawarwari masu fa’ida da sabbin dabaru don ci gaba,” inji gwamnan.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp