Home General Kotu ta dakatar da gudanar da zaben ƙananan hukumomi a jihar Kano

Kotu ta dakatar da gudanar da zaben ƙananan hukumomi a jihar Kano

Babbar kotun tarayya a Najeriya ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kano gudanar da zaben ƙananan hukumomi.

Mai shari’a Simon Ameboda ne ya dakatar da hukumar gudanar da zaben da ake shirin yi a jihar.

A hukuncin da alƙalin kotun ya yanke ya ce naɗin da aka yi na shugabancin hukumar zabe a jihar da sauran shugabbanni ya saba da kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, saboda suna ɗauke da katin jamiyyar NNPP.

Alƙalin ya ce naɗin shugabannin hukumar ya saba da sashi na 199(1) da sashi na 200(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya da aka yiwa gyara a 1999.

Har wa yau kotun ta ce naɗin ya saba da sashi na 4(b) na dokokin hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano.

Kotun tace hukumar zabe a yanzu ba za ta iya gudanar da zabe ba, duba da yadda aka karya ƙa’idojin naɗin shugabannin hukumar.

Kotun ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC kada ta bawa hukumar zabe mai zaman kanta ta Kano KANSIEC kayan da za ta yi amfani da su wurin gudanar da zabe har sai an bi dukkanin dokoki da ƙa’idoji wurin samar da shugabancin hukumar.

Kafin hukuncin kotun na yau an shirya yin zaben ƙananan hukumomin jihar Kano ne a ranar Asabar mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp