Home General Kotu ta dakatar da gudanar da zaben ƙananan hukumomi a jihar Kano

Kotu ta dakatar da gudanar da zaben ƙananan hukumomi a jihar Kano

Babbar kotun tarayya a Najeriya ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kano gudanar da zaben ƙananan hukumomi.

Mai shari’a Simon Ameboda ne ya dakatar da hukumar gudanar da zaben da ake shirin yi a jihar.

A hukuncin da alƙalin kotun ya yanke ya ce naɗin da aka yi na shugabancin hukumar zabe a jihar da sauran shugabbanni ya saba da kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, saboda suna ɗauke da katin jamiyyar NNPP.

Alƙalin ya ce naɗin shugabannin hukumar ya saba da sashi na 199(1) da sashi na 200(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya da aka yiwa gyara a 1999.

Har wa yau kotun ta ce naɗin ya saba da sashi na 4(b) na dokokin hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano.

Kotun tace hukumar zabe a yanzu ba za ta iya gudanar da zabe ba, duba da yadda aka karya ƙa’idojin naɗin shugabannin hukumar.

Kotun ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC kada ta bawa hukumar zabe mai zaman kanta ta Kano KANSIEC kayan da za ta yi amfani da su wurin gudanar da zabe har sai an bi dukkanin dokoki da ƙa’idoji wurin samar da shugabancin hukumar.

Kafin hukuncin kotun na yau an shirya yin zaben ƙananan hukumomin jihar Kano ne a ranar Asabar mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp