Home General Kotu ta dakatar da gudanar da zaben ƙananan hukumomi a jihar Kano

Kotu ta dakatar da gudanar da zaben ƙananan hukumomi a jihar Kano

Babbar kotun tarayya a Najeriya ta dakatar da hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Kano gudanar da zaben ƙananan hukumomi.

Mai shari’a Simon Ameboda ne ya dakatar da hukumar gudanar da zaben da ake shirin yi a jihar.

A hukuncin da alƙalin kotun ya yanke ya ce naɗin da aka yi na shugabancin hukumar zabe a jihar da sauran shugabbanni ya saba da kundin tsarin mulkin Najeriya na 1999, saboda suna ɗauke da katin jamiyyar NNPP.

Alƙalin ya ce naɗin shugabannin hukumar ya saba da sashi na 199(1) da sashi na 200(1) na kundin tsarin mulkin Najeriya da aka yiwa gyara a 1999.

Har wa yau kotun ta ce naɗin ya saba da sashi na 4(b) na dokokin hukumar zabe mai zaman kanta ta jihar Kano.

Kotun tace hukumar zabe a yanzu ba za ta iya gudanar da zabe ba, duba da yadda aka karya ƙa’idojin naɗin shugabannin hukumar.

Kotun ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta ta Najeriya INEC kada ta bawa hukumar zabe mai zaman kanta ta Kano KANSIEC kayan da za ta yi amfani da su wurin gudanar da zabe har sai an bi dukkanin dokoki da ƙa’idoji wurin samar da shugabancin hukumar.

Kafin hukuncin kotun na yau an shirya yin zaben ƙananan hukumomin jihar Kano ne a ranar Asabar mai zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 200 Sun Mutu Sakomakon Girgizar ƙasar a ColombiaShahararren Mawaƙin Najeriya, Davido ya Rubuta wa Trump Wasiƙa Kan Zaɓen Jihar OsunHukumar NHRC ta Buƙaci a Kama Malamin Addinin, Sheikh JingirRundunar sojin Najeriya ta Daƙile Shirin Ƴan Bindiga a FilatoJami'an Ƴan Sanda 10 Sun Mutu Yayin Artabu da Ƴan Bindiga a Jihar KebbiAn Naɗa ɗan Najeriya Gidado Shuaib Wakilin Matasa na IPRA-UN Gabanin GWAEFCC da "Wuce Gona da Iri" da Tambayar 2027: Shin ana Rudar da Tinubu ta Hanyar Mutanen da ke Kewaye da Shi ? Daga Yushau A. ShuaibAn Samu Gawar Yara 3 da guda 1 a Sume a Gidan Mai Maganin GargajiyaMene ne Ainihin Abin da ya faru Aka Rufe Asusun Bankunan Gwamnatin Osun ?Jami'an Tsaro Sun Ceto Mutane 308 a Jihohin Arewacin Najeriya An Kama Mutane 6 da Ake Zargin da Taimaka wa Mayaƙan ISWAP a Jihar BornoZaɓen 2027: PDP ta Miƙa Sunan Jonathan ga INEC a Matsayin ɗan Takararta na Shugaban ƙasaIyanen Babban Jami'in Kula da Harkokin Kuɗaɗen ƙungiyar ISWAP Sun Miƙa Wuya ga SojojiAna Zargin Mayaƙan Boko Haram da Kashe Sojojin Nijar 14Gombe 2027: Malamai da Mambobin APC Sun yi Allah-wadai da Sukar Rarara ga Pantami
X whatsapp