Home Labarai Sojojin Najeriya biyar sun mutu a haɗarin mota a jihar Filato

Sojojin Najeriya biyar sun mutu a haɗarin mota a jihar Filato

Wasu sojojin sama na Najeriya biyar na daga cikin matafiya 19 da suka rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya auku a Hawan Kibo da ke ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato a jiya Talata.

A wata sanarwa da kakakin rundunar sojin sama ta Najeriya, Olusola Akinboyewa ya fitar, ya ce, sojojin na kan hanyarsu ne ta zuwa wani wasa a Abuja, lokacin da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota.

Sai dai kuma wani bayani da hukumar kiyaye haɗura ta Najeriya ta fitar ya saɓa da wanda kakakin sojin ya fitar, inda hukumar ta ce motar bas ta sojojin ƙirar Hiace, mai ɗaukar mutum 18 da ta taso daga Yola ta bi yo ta Jos a kan hanyarta ta zuwa Abuja ta ci karo ne da tirela wadda ke tsaye a kan hanya, lamarin da ya janyo mutuwar direban da dukkanin sauran mutanen da ke cikin motar su 18.

A wata hira da tasahar talabijin ta Channels, kakakin hukumar ta kiyaye haɗura (FRSC) a jihar ta Filato, Peter Longsan, ya ce dukkanin mutanen da ke cikin wannan mota bas da sojojin suke sun mutu.

Longsan ya danganta munin haɗarin da ya kai ga mutuwar mutanen gaba ɗaya, da gudun da direab bas ke yi inda ya ce a dalilin hakan ne da ta yi karo da tirelar ba wanda ya tsira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp