Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta hana fitar da gas din girki kasashen waje

Gwamnatin Nijeriya ta hana fitar da gas din girki kasashen waje

Gwamnatin Najeriya ta hana fitar da gas ɗin girki zuwa ƙasashen waje, daga ranar 1 ga watan Nuwamba mai kamawa, a wani mataki da ta ce ta ɗauka domin hana hauhawara farashin gas ɗin.

Ƙaramin ministan albarkatun mai mai kula da harkokin gas, Ekperikpe Ekpo, ne ya bayyana haka, a cikin irin matakan da ya ce gwamnati ta ɗauka domin tabbatar da saukinsa.

Ministan ya nuna damuwarsa kan yadda farashin gas ɗin ke ta hauhawa a baya-bayan nan daga tsakanin naira 1,100 da 1,250 zuwa naira 1,500 a kan kilo ɗaya.

A kan hakan ministan ya yi taro da masu ruwa da tsaki a kan gas ɗin a Abuja ranar Talata kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, domin lalubo hanyoyin magance matsalar hauhawara farashin, wadda ke damun ‘yan ƙasar.

A nan ne ministan ya sanar da cewa daga cikin muhimman matakan da aka ɗauka sun haɗa da umartar kamfanin mai na ƙasar NNPCL da masu samar da gas ɗin na cikin ƙasa da su daina fitar da gas ɗin da aka samar a ƙasar zuwa waje.

Ekpo ya jaddada buƙatar ganin an samar da wani tartibin tsari na tsayar da farashin gas ɗin wanda zai dace da cikin gida.

A wata sanarwa da kakakin ministan, Louis Ibah, ya fitar ya ce an bai wa hukumomin da ke aikin hakowa da sayar da albarkatun mai na ƙasar da su fitar da wani tartibin tsarin farashin gas ɗin na cikin gida nan da kawana 90.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp