Home Labarai Gwamnatin Nijeriya ta hana fitar da gas din girki kasashen waje

Gwamnatin Nijeriya ta hana fitar da gas din girki kasashen waje

Gwamnatin Najeriya ta hana fitar da gas ɗin girki zuwa ƙasashen waje, daga ranar 1 ga watan Nuwamba mai kamawa, a wani mataki da ta ce ta ɗauka domin hana hauhawara farashin gas ɗin.

Ƙaramin ministan albarkatun mai mai kula da harkokin gas, Ekperikpe Ekpo, ne ya bayyana haka, a cikin irin matakan da ya ce gwamnati ta ɗauka domin tabbatar da saukinsa.

Ministan ya nuna damuwarsa kan yadda farashin gas ɗin ke ta hauhawa a baya-bayan nan daga tsakanin naira 1,100 da 1,250 zuwa naira 1,500 a kan kilo ɗaya.

A kan hakan ministan ya yi taro da masu ruwa da tsaki a kan gas ɗin a Abuja ranar Talata kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito, domin lalubo hanyoyin magance matsalar hauhawara farashin, wadda ke damun ‘yan ƙasar.

A nan ne ministan ya sanar da cewa daga cikin muhimman matakan da aka ɗauka sun haɗa da umartar kamfanin mai na ƙasar NNPCL da masu samar da gas ɗin na cikin ƙasa da su daina fitar da gas ɗin da aka samar a ƙasar zuwa waje.

Ekpo ya jaddada buƙatar ganin an samar da wani tartibin tsari na tsayar da farashin gas ɗin wanda zai dace da cikin gida.

A wata sanarwa da kakakin ministan, Louis Ibah, ya fitar ya ce an bai wa hukumomin da ke aikin hakowa da sayar da albarkatun mai na ƙasar da su fitar da wani tartibin tsarin farashin gas ɗin na cikin gida nan da kawana 90.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
HURIWA ta Soki Ƴan Sanda da NDPC Kan Jinkirin Binciken Zargin Kutse da aka yi wa Bayanan NIPSS da ya Shafi Jami’in Sojan RuwaƳa'yan El-Rufai Sun Shiga Rikici Yayin da Bashir ya Zargi Bello da Shan Muggan Kwayoyi da Cin Amanar suTsaro, Fafutuka da Nauyin Tabbatarwa Daga Mukhtar Ya’u MadobiONSA ta Fitar da Faɗakarwar Tsaro, ta Bukaci Ƴan Najeriya su ƙara Yawan Tsawaita TsaroHukumar DSS ta Dakatar da Shari'ar Sowore Kan Laifukan Intanet Har Sai Bayan Zaben Shugaban Kasa na 2027Gwarzo ya ba da Gudummuwar ₦10m ga Horarwa na Musamman na PRNigeria Bayan ya ba da Gidansa na Abuja Don Cibiyar Koyon Aikin Jarida2027: Bayan Takardu da Sauran Tsoffin Maganganu Marasa Amfani, ‘Yan Najeriya Sun Cancanci Kamfen Din da Ya Dace Da Matsaloli  Daga Kabir AkintayoGwamnati Tarayya ta Bayyana Bas 100 Masu Amfani da Wutar Lantarki Don Rage Wa Ma’aikatan Gwamnati Matsalar SufuriƳan Ta’adda na Amfani da Kafafen Sada Zumunta da Dandamalin Aikin Tura Kuɗi Don Tallafa Wa Ayyukansu — BukartiBinciken Gaskiya na PRNigeria: Ta Karyata Da’awar Tony Elumelu ta Cewa An yi Satar Man Fetur Kashi 97% Kafin Zamanin TinubuMeyasa Mutuwar Bazata Take Daukar Masu Alheri ta Bar Mugaye ? Na Yushau A. ShuaibSojoji Sun Kama Bindigar AK-103 Da Aka Boye a Cikin Jakar Gero, Sun Kama Mutum Uku A ZamfaraSojoji Sun Kama Shahararren Shugaban Ƴan Bindiga, 'Sanusi Maigilas' a Dajin Katsina2027: Yadda Zan Magance Rashin Tsaro, In Magance Matsalolin Tattalin Arziki da Zamantakewa a Kwara — Zakari MohammedLabarin NIPSS Mai Damuwa: Lokacin da Jami'in Sojan Ruwa Ya Cin Zarafin Mawallafi Daga Nuhu Mohammed
X whatsapp