Home General Gwamnatin Najeriya za ta hukunta jihohin da suka ƙi zaɓen ƙananan hukumomi

Gwamnatin Najeriya za ta hukunta jihohin da suka ƙi zaɓen ƙananan hukumomi

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta ɗauki mataki a kan jihohin da suka ƙi gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi da zai tabbatar da cin gashin kai na ƙananan hukumomin kamar yadda kotun ƙolin ta zartar.

Babban lauyin gwamnatin tarayyar Mista Lateef Fagbemi, wanda ya bayyana hakan a jihar Ekiti a jiya Talata, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito ya ce ba gudu ba ja da baya a kan shirin aiwatar da hukuncin kotun ƙolin kan cin gashin ƙananan hukumomin.

Mista Fagbemi ya ce gwamnatin za ta yi nazarin dokokin jihohi a kan zaɓen ƙananan hukumomi tare da duba dalilin da ya sa wasu jihohinke jinkirin gudanar da zaɓen.

Bayanai sun nuna cewa a yanzu sama da ƙananan hukumomi 164 ne a jihohi takwas ba su yi zaben ba.

Jaridar ta kuma ruwaito cewa, wasu rahotanni na nuna cewa wataƙila Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da hukuncin kotun ƙolin a kan cin gashin kai na ƙananan hukumomi nan da ƙarshen watan nan na Oktoba.

Hakan na nufin gwamnatin tarayyar za ta iya riƙe kason kuɗin ƙananan hukumomin da ba a yi zaɓe ba, kamar yadda hukuncin kotun ya ayyana.

Ƙananan hukumomin da ba a yi zaɓe ba na jihohin Katsina da Zamfara da NasarawaOndo, da Osun da Ogun da Cross Rivers.

Hukuncin kotun ya nuna cewa, saɓa doka ne gwamnonin jihohi su ci gaba da karɓa ko riƙe kason kuɗaɗen ƙananan hukumomi a ƙarƙashin asusun haɗin gwiwa na jida da ƙananan hukumomi.

Wasu gwamnonin jihohin ƙasar dai na ganin wallen hukuncin kotun.

A makon da ya wuce gwamnan jihar Anambra Farfesa Chukuma Soludo, a lokacin sanya hannu kan dokar mulkin ƙananan hukumomi ya yi gargaɗin cewa ba wa ƙananan hukumomin ƙasar 774 cikakken ƴancin cin gashin kai ka iya haifar da abin da ya kira ”gagarumar matsala” ta yarda za a kasa samar da cigaba mai ɗorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp