Home General Gwamnatin Najeriya za ta hukunta jihohin da suka ƙi zaɓen ƙananan hukumomi

Gwamnatin Najeriya za ta hukunta jihohin da suka ƙi zaɓen ƙananan hukumomi

Gwamnatin tarayyar Najeriya ta ce za ta ɗauki mataki a kan jihohin da suka ƙi gudanar da zaɓen ƙananan hukumomi da zai tabbatar da cin gashin kai na ƙananan hukumomin kamar yadda kotun ƙolin ta zartar.

Babban lauyin gwamnatin tarayyar Mista Lateef Fagbemi, wanda ya bayyana hakan a jihar Ekiti a jiya Talata, kamar yadda jaridar Daily Trust ta ruwaito ya ce ba gudu ba ja da baya a kan shirin aiwatar da hukuncin kotun ƙolin kan cin gashin ƙananan hukumomin.

Mista Fagbemi ya ce gwamnatin za ta yi nazarin dokokin jihohi a kan zaɓen ƙananan hukumomi tare da duba dalilin da ya sa wasu jihohinke jinkirin gudanar da zaɓen.

Bayanai sun nuna cewa a yanzu sama da ƙananan hukumomi 164 ne a jihohi takwas ba su yi zaben ba.

Jaridar ta kuma ruwaito cewa, wasu rahotanni na nuna cewa wataƙila Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya aiwatar da hukuncin kotun ƙolin a kan cin gashin kai na ƙananan hukumomi nan da ƙarshen watan nan na Oktoba.

Hakan na nufin gwamnatin tarayyar za ta iya riƙe kason kuɗin ƙananan hukumomin da ba a yi zaɓe ba, kamar yadda hukuncin kotun ya ayyana.

Ƙananan hukumomin da ba a yi zaɓe ba na jihohin Katsina da Zamfara da NasarawaOndo, da Osun da Ogun da Cross Rivers.

Hukuncin kotun ya nuna cewa, saɓa doka ne gwamnonin jihohi su ci gaba da karɓa ko riƙe kason kuɗaɗen ƙananan hukumomi a ƙarƙashin asusun haɗin gwiwa na jida da ƙananan hukumomi.

Wasu gwamnonin jihohin ƙasar dai na ganin wallen hukuncin kotun.

A makon da ya wuce gwamnan jihar Anambra Farfesa Chukuma Soludo, a lokacin sanya hannu kan dokar mulkin ƙananan hukumomi ya yi gargaɗin cewa ba wa ƙananan hukumomin ƙasar 774 cikakken ƴancin cin gashin kai ka iya haifar da abin da ya kira ”gagarumar matsala” ta yarda za a kasa samar da cigaba mai ɗorewa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp