Home Labarai Gwamnatin Kano ta dakatar da ƴanjarida 14 daga aiki a gidan gwamnati

Gwamnatin Kano ta dakatar da ƴanjarida 14 daga aiki a gidan gwamnati

Gwamnatin jihar Kano ta dakatar da ƴan-jarida 14 da ke aiki a fadar gwamnatin jihar daga aiki tare da neman sauyinsu daga hukumomin da suke ƙarƙashinsu.

A wani saƙo da kakakin gwamnan jihar, Sanusi Bature Dawakin Tofa, ya fitar ga waɗanda abin ya shafa, ya umarce su da su koma wuraren aikinsu, tare da neman hukumominsu su aika da wasu da za su maye gurbinsu a gidan gwamnatin jihar.

Babu wani dalili da kakakin ya bayyana na ɗaukar wannan mataki, illa dai ya buƙace su da su bi umarnin wanda ya fara aiki daga yau Talata.

To amma a saƙon da ya rubuta a shafin WhatsApp na tawagar ‘yanjaridar da ke aiki a fadar gwamnatin jihar ta Kano, Sanusin ya bayyana cewa : ”Abin takaici a lokacin da na yi tafiya zuwa ƙasar Serbia a makon da ya gabata, wasu abubuwa sun faru, saboda haka akwai buƙatar shugabancin a wannan mawuyacin hali ya ɗauki mataki…”

Wasu daga cikin ƴanjaridar da abin ya shafa sun haɗa da na kafofin yaɗa labarai na gwamnatin jihar da na tarayya da kuma masu zaman kansu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp