Home Labarai Bukola Saraki ya taya wankwaso murnar cika shekaru 68

Bukola Saraki ya taya wankwaso murnar cika shekaru 68

Tsohon shugaban majalisar dattawa ta ƙasa, Dr. Abubakar Bukola Saraki, ya ce tsohon gwamnan jihar Kano Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso kwararre ne wajen iya jagoranci.

Saraki ya bayyana haka ne a saƙon taya Kwankwaso murnar cika shekara 68 da haihuwa a yau 21-10-2020.

A cikin wata sanarwa da mataimakinsa a kan kafafen yada labarai, Abba Gwale ya fitar, Saraki, ya bayyana Kwankwaso a matsayin ɗan uwa kuma aboki wanda kuma ya kware wajen iya jagoranci.

 

“Abokina kuma ɗan uwana, tsohon gwamnan jihar Kano kuma jagoran Kwankwasiyya, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso ya kasance ƙwararren ɗan siyasa kuma jagora na gari.

 

“A yau da yake murnar zagayowar ranar haihuwarsa, ina taya iyalansa da ƴan uwansa da mabiyansa murnar wannan rana, sannan ina roƙon Allah ya ci gaba da ƙarfafa masa gwiwa, ya bashi cikakkiyar lafiya da basira da tsawon rai”. Inji Saraki.

Saraki da Kwankwaso dai sun yi aiki tare a majalisa ta takwas, a lokacin da Sarakin, wanda shima tsohon gwamnan jihar Kwara ne, yake matsayin shugaban majalisar dattawa daga shekara ta 2015 zuwa 2019, lokacin mulkin tsohon shugaban kasa Muhammad Buhari.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mutane 6 Sun Rasu 4 Sun Jilkata Sanadiyyar Tsawa a Jihar AdamawaMatatar Dangote ta Dakatar da Amfani da Naira Wajen Sayar da Man FeturZaɓen 2027: Jam'iyyar ADC ta Mayar da Martani kan Hukuncin Kotu Akwai Yiwuwar ba zan kai Lokacin Zaɓen 2027 ba - ObiHukuncin da Kotu ta Yanke wa Direban Keke Napep Kan Aikata Fyaɗeɓata Sunan Gwamnatin Katsina: Kotu ta buƙaci Ƴan Sanda su Tsare Dr Kurfi Gwamnonin Arewacin Najeriya sun Kafa Gidauniyar Yaƙi da Matsalar TsaroGwamnatin Tarayya ba ta Yanke Hukuncin Sauya Kayan NYSC ba - Ministan MatasaJuyin Mulki: DSS ta Gurfanar da Mutane 5 kan ɓoye Timipre Sylva Ƴan Bindiga Sun Kashe Mutane 2 Tare da Limami a Jihar Sokoto Dakarun Soji Sun Bankaɗo Wajen ƙera da Rarraba Bindigogi ga Ƴan Ta'addaJami'an DSS Sun Kama Tsohon Ministan Kimiyya da Fasaha, Uche NnajiYan Bindiga Sun Hallaka Mutane 10 a Jihar BenueNMDPRA ta Gargaɗi Gidajen Man da ba su Rage Farashi ba NECO: ɗalibai 35 na Hannun Ƴan Bindiga - Ƴan Sanda 
X whatsapp