Home General Sojojin Nijeriya sun Jajjada biyayyarsu ga Tinubu

Sojojin Nijeriya sun Jajjada biyayyarsu ga Tinubu

Hedikwatar tsaron Najeriya ta gargaɗi ɗaiɗaikun mutane da ƙungiyoyi da ke kira ga sojoji su yi juyin mulki a ƙasar, tare da jaddada cewa yin hakan cin amanar ƙasa ne a ƙarƙashin kundin tsarin mulki.

Wannan na ƙunshe ne a wata sanarwa da darektan yada labarai na hedikwatar tsaron, Birgediya Janar Tukur Gusau ya fitar, inda ya ce sojojin za su ci gaba da mayar da hankali a kan babban aikin da ya wajaba a kansu, wanda ya haɗa da kare yankin ƙasar tare da tabbatar da zaman lafiya da tsaro.

Hukumomin sojin sun kuma ƙara jaddada biyayyarsu ga gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu tare da ƙudurinsu na kare tsarin dumukuraɗiyya a ƙasar.

Darektan ya ƙara da cewa ya kamata masu neman sojoji su yi juyin mulki, kamar yadda aka gani a wani hoton bidiyo da ake ta yaɗawa, su sani cewa wannan abu cin amanar ƙasa ne a bisa tanadin kundin tsarin mulki.

Janar Gusau, ya kuma ce zaman lafiyar da aka samu a ƙasar a yanzu, ya samu ne sakamakon goyon bayan da shugaban ƙasar ke ba wa sojoji da kuma jajircewar shugabancin sojojin.

Ya kuma bayar da tabbacin cewa sojojin tare da haɗin gwiwar sauran jami’an tsaro za su ɗauki dukkanin matakan da suka dace wajen hana duk wani yunƙuri na sauyin da ta hanyar kundin tsarin mulki ba.

Hedikwatar tsaron ta Najeriya ta fitar da wannan sanarwa ne, bayan da aka riƙa yaɗa wani hoton bidiyo a kwakin nan inda wasu ke kira ga sojoji su yi juyin mulki a Najeriyar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp