Home Labarai Wani babban kwamandan RSF ya miƙa wuya ga sojojin Sudan

Wani babban kwamandan RSF ya miƙa wuya ga sojojin Sudan

Rundunar sojin Sudan ta ce ɗaya daga cikin kwamandan mayakan rundunar RSF Abuagla Keikal, ya miƙa wuya tare da wasu dakarunsa, wanda shi ne na farko da aka sami wani babban jami’inta da yayi, tun bayan da ɓangarorin suka faro rikici a tsakiyar watan Afrelun shekarar da ta gabata.

Rundunar sojojin Sudan wacce a ƴan kwanakin nan ta bayar da rahotan fara samun nasarar kwato wasu yankuna na babban birnin ƙasar Khartoum, ta ce Keikal ya ɗauki matakin ne sakamakon yadda rundunar RSF ta sauka daga kan tsarin da aka samar da ita.

Wasu daga cikin masu goyon bayan sojojin Sudan, sunta saka hotunan Keikal da ke jagorantar rundunar RSF a kudu maso gabashin jihar El Gezira, a kafofin sada zumunta, bayan sanar da matakin da ya ɗauka.

Kawo yanzu dai rundunar RSF da ta kwace iko da sassan ƙasar da dama da kuma shi kansa Keikal, basu ce komai game da lamarin ba.

Rikicin na Sudan ya sanya sama da mutane miliyan 10 barin muhallansu tare da jefa wasu da dama cikin matsananciyar yunwa, lamarin da ya sanya Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce yakin da ake gwabzawa a Sudan din tsakanin sojoji da dakarun RSF,  ya haifar da ɗaya daga cikin matsalolin ayyukan jin kai mafi muni a duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Fasinjoji 18 Sun Mutu a Hatsarin Mota Yayin Dawowa Daga LegasGwamnatin Najeriya ta ƙudiri Anyiar Tara N2.5trn Daga Kuɗaɗen Shiga a 2026Wanda ya Kafa PRNigeria ya Nufi Kotu Don Daukaka Kara Kan Watsi da Karar ₦1bn da ya Shigar Kan NIPSSObi ya yi Tsokaci Game da Hukuncin da Kotu ta yi na Soke Rijistar Jam'iyyar NDC Soke Rijistar NDC Murƙushe Dimokuraɗiyya ne - PDPAn Gurfanar da ƙarin Mutane 17 kan Kashe Matar Aure a Jihar KadunaCutar Tamowa: Gwamnatin Kebbi ta Karyata Rahoton MSF Kan Mutuwar ƙananan  Yara a JiharJam'iyyar NDC ta Magantu Bayan Kotu ta Soke Rijistar taAbinda Ke Haddasa Matsalolin Tsaro a Jihar mu - Gwamnan Ahmed Aliyu Babban Bankin Najeriya ya Umarci Bankuna da su Rufe Asusun Mutane da Ake Zargin da Tallafawa Ta'addaci Sunayen Mutane 6 da Kamfanonin Canji 3 da Ake Zargin da Tallafa wa Ta'addaci a Najeriya Mun Ceto Mutane 47 Daga Hannun Mayaƙan ISWAP - Rundunar Sojin NajeriyaSanatocin za su Fara Duba ƙudirin  Kafa ƴan Sandan Jihohi Ranar Laraba - AkpabioMatakin da Amurka ta ɗauka na Cire Tallafin Cutar HIV a Afirka ta Kudu Zai Janyo Asarar Rayuka - MDDAn Gurfanar da Mutane 24 Bisa Zargin Kashe Matar Aure a Maraban Jos
X whatsapp