Home Labarai Wani babban kwamandan RSF ya miƙa wuya ga sojojin Sudan

Wani babban kwamandan RSF ya miƙa wuya ga sojojin Sudan

Rundunar sojin Sudan ta ce ɗaya daga cikin kwamandan mayakan rundunar RSF Abuagla Keikal, ya miƙa wuya tare da wasu dakarunsa, wanda shi ne na farko da aka sami wani babban jami’inta da yayi, tun bayan da ɓangarorin suka faro rikici a tsakiyar watan Afrelun shekarar da ta gabata.

Rundunar sojojin Sudan wacce a ƴan kwanakin nan ta bayar da rahotan fara samun nasarar kwato wasu yankuna na babban birnin ƙasar Khartoum, ta ce Keikal ya ɗauki matakin ne sakamakon yadda rundunar RSF ta sauka daga kan tsarin da aka samar da ita.

Wasu daga cikin masu goyon bayan sojojin Sudan, sunta saka hotunan Keikal da ke jagorantar rundunar RSF a kudu maso gabashin jihar El Gezira, a kafofin sada zumunta, bayan sanar da matakin da ya ɗauka.

Kawo yanzu dai rundunar RSF da ta kwace iko da sassan ƙasar da dama da kuma shi kansa Keikal, basu ce komai game da lamarin ba.

Rikicin na Sudan ya sanya sama da mutane miliyan 10 barin muhallansu tare da jefa wasu da dama cikin matsananciyar yunwa, lamarin da ya sanya Majalisar Ɗinkin Duniya ta ce yakin da ake gwabzawa a Sudan din tsakanin sojoji da dakarun RSF,  ya haifar da ɗaya daga cikin matsalolin ayyukan jin kai mafi muni a duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp