Home Labarai Gwamna Kano ya taya Kwankwaso murna cika shekaru 68 a duniya

Gwamna Kano ya taya Kwankwaso murna cika shekaru 68 a duniya

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf taya mai gidansa sanata Rabi’u Musa Kwankwaso murnar cika shekaru 68 a duniya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikewa manema labarai a jihar.

Cikin Wani Sako da Gwamnan ya Wallafa a Shafinsa na Sada zumunta Wanda ya dauki hankali Al’umma musamman Yan Siyasa dake Tabbatar da biyayya ga Mai Gidansa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

“Ya zama wajibi na mika sakon Taya murna kasancewar ka a matsayin jagora kuma shugaba wanda na yi aiki da kai tsawon shekaru 38 da suka wuce”. Inji Gwamnan

Gwamnan ya kara da cewa “lokacin da na yi aiki da Kwankwaso na koyi abubawa da dama wadanda suka taimake ni a Rayuwa dan haka na ke mika sakon taya Murnar zagayowar ranar haihuwar Mai gidana Shekaru 68 a Duniya”.

Kwankwaso Wani jigo ne a Siyasa a Kasar nan Wanda Yake da Wasu Muhimman abubuwan koyi na Cigaba ga Al’ummar Kasar nan a cewar Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Ya ce a madadin shi Kansa da iyalansa, gwamnati da al’ummar jihar Kano yana taya tsohon gwamnan murnar cika shekaru 68 a duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Mayaƙan Lakurawa Sun Kashe Sojoji 7 a SokotoAn faɗa wa Shugaba Tinubu Cewa Ina Kitsa Yadda Zan Kashe Shi - ShettimaRundunar 'Yan Sandan Najeriya ta Ceto ƴan Mali 30 Daga Hannun Masu Safarar MutaneMun Kashe Mayaƙan ISIS 175 - Rundunar Sojin NajeriyaFarfesa Pantami ya Janye Daga Takarar Gwamnan Jihar GombeKishiya: Tsakanin ONSA na Ribadu da Tsaron Gida Famadewa Daga Yushau A. ShuaibZaben Fidda Gwani: An Harbe Mutum a Jihar PlateauRundunar 'Yan Sanda ta Tabbatar Kashe Jami'anta 17 a YobeSatar Kayayyakin Banki: An Kama Mutane Huɗu a Jihar Gombe'Yan Bindiga Sun Sace Basarake Tare da Mata 2 a KatsinaJami'an Kwastam Biyu sun Rasa Ransu a Fafatawa da LakurawaMatar Aure ta Zuba wa Kishiyarta da 'Ya'yanta Biyu Fetur Tare da Banka Musu Wuta a KanoIna da ƴancin Mu'amala da Kowa ba Tare da La'akari da Jam'iyya ba - WikeAdadin Masu Fama da Cutar Tamowa na ƙaruwa a Najeriya - MSFGwamnatin Yobe ta Sha Alwashin Kawo ƙarshen Hare-Haren Boko Haram
X whatsapp