Home Labarai Gwamna Kano ya taya Kwankwaso murna cika shekaru 68 a duniya

Gwamna Kano ya taya Kwankwaso murna cika shekaru 68 a duniya

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf taya mai gidansa sanata Rabi’u Musa Kwankwaso murnar cika shekaru 68 a duniya.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Kano Sanusi Bature Dawakin Tofa ya aikewa manema labarai a jihar.

Cikin Wani Sako da Gwamnan ya Wallafa a Shafinsa na Sada zumunta Wanda ya dauki hankali Al’umma musamman Yan Siyasa dake Tabbatar da biyayya ga Mai Gidansa Sanata Rabiu Musa Kwankwaso.

“Ya zama wajibi na mika sakon Taya murna kasancewar ka a matsayin jagora kuma shugaba wanda na yi aiki da kai tsawon shekaru 38 da suka wuce”. Inji Gwamnan

Gwamnan ya kara da cewa “lokacin da na yi aiki da Kwankwaso na koyi abubawa da dama wadanda suka taimake ni a Rayuwa dan haka na ke mika sakon taya Murnar zagayowar ranar haihuwar Mai gidana Shekaru 68 a Duniya”.

Kwankwaso Wani jigo ne a Siyasa a Kasar nan Wanda Yake da Wasu Muhimman abubuwan koyi na Cigaba ga Al’ummar Kasar nan a cewar Gwamna Abba Kabir Yusuf.

Ya ce a madadin shi Kansa da iyalansa, gwamnati da al’ummar jihar Kano yana taya tsohon gwamnan murnar cika shekaru 68 a duniya.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Shin AtikuObi Zasu Iya Tsige TinubuShettima a 2027? Daga Yushau A. ShuaibYadda Shari'ar Masarautar Kano ke Ci gaba da Wakana a Kotun ta ƙoliTawagar Amurka na Shirin Tafiya Pakistan Domin Tattaunawar Sulhu da IranDole Najeriya ta Samu Tsaro ta Kowane Hali - Babban Hafsan TsaroChelsea da Newcastle na Harin Coulibaly, Liverpool na Neman Siyan Marcos SensiBadaƙalar $1.3m: Kotu ta ba EFCC izinin Kama Tsohuwar Ministar jin ƙan Najeriya Sadiya FarouqRaphinha ya Magantu kan Fitar da ƙungiyarsa da aka yi Daga Champion LigRundunar sojin Najeriya ta Musanta bai wa Tsofaffin Mayaƙan Boko Haram MakamaiGwamnatin Tarayya ta Sauya Zarge-Zargen da ta ke yi wa MalamiAn Binne Birgediya Janar Braimah da Sauran Sojojin da Boko Haram ta KasheYaƙin Iran: Hauhawar farashin Kaya a Najeriya ya ƙaruAdadin Matasa 'Yan kwaya da Muka Kama a Shekara 5 - NDLEAJam'iyyar ADC ta Kori Nafi'u Bala GombeRigakafin ƙyanda ya Ceci Yara Miliyan 20 a Afirka - Hukumar Lafiya ta Duniya2027 Ita ce Dama ta ƙarshe da zan Fito Takara - Atiku
X whatsapp