Home General KEDCO ta Hakurkurtar da abokan Huldarta na Kano, Katsina da Jigawa

KEDCO ta Hakurkurtar da abokan Huldarta na Kano, Katsina da Jigawa

Kamfanin rarraba hasken wutar lantarki dake lura da shiyyar Kano, jigawa da katsina KEDCO ta nemi afuwar abokan huldarta bisa karancin wutar da aka samu a ‘yan tsakanin nan.

kamfanin ta bayyana hakan ne ta bakin shugaban dake lura da sashen raba wutar lantarki na shiyyar, Engr. Kasim Abdullahi Burkullo a yayin da yake ganawa da manema labarai a shalkwatar hukumar dake jihar Kano.

Wannan dai na zuwa ne a daidai lokacin da Majalisar Wakilan Najeriya ta umarci kwamitinta da ke kula da harkokin wutar lantarki ya gudanar da bincike kan matsalar yawan lalacewar layin samar da lantarki na ƙasar, ya kuma bayar da rahoto cikin mako uku.

Matakin ya biyo bayan amincewa da buƙatar da ɗan majalisar Mansur Mano Soro, daga jihar Bauchi ya gabatar a zamanta na yau Laraba.

Ɗan majalisar ya bayyana damuwa kan matsalar lalacewar layin lantarkin na ƙasa da ta ƙi ci ta ƙi cinyewa a kwanakin nan, lamarin da ke jefa ƙasar cikin rashin wuta tare da jefa ‘yan ƙasar cikin matsin rayuwa da suke fama da shi.

Ya ce, wutar lantarki aba ce da ta zama wajibi wajen bunƙasar tattalin arziƙi da kuma cigaban duk wata ƙasa.

Hon. Mansur ya nuna takaicinsa yadda aka samu matsalar lalacewar layin wutar na ƙasa sau takwas a cikin wannan shekara ta 2024 kaɗai, inda ya bayyana hakan a matsayin abin damuwa da takaici.

Ɗan majalisar ya ce sakamakon matsalar lalacewar, gaba ɗaya yankin arewa maso yamma da kuma arewa maso gabas na ƙasar sun kasance cikin duhu, da uwa uba ƙarin tsanani na tsadar rayuwa.

Ya ƙara da cewa abin takaici ne yadda matsalar ke faruwa a daidai lokacin da ministan wutar lantarkin ke ba wa ‘yan Najeriya tabbacin ingancin samar da wutar, abin da ya sa har gwamnati ta ce ya sa dole ta ƙara kuɗin wutar ga masu amfani da ita na rukunin farko ko babban layi (Band A).

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Dangote ya ƙara farashin man feturHukumar Jin dadin alhazan Kano ta sanar da ranar fara jigilar maniyatantaYadda Lakurawa suka kashe masallata a KebbiDSS ta kama jagoran ISWAP da ake nema ruwa a jallo a EdoBa mu taɓa goyon bayan musguna wa Kristoci ba - Gwamnatin NajeriyaGobara ta tashi a babban kasuwar Fika da ke jihar YobeWaye Tunji Disu: Sabon Babban Sifeton 'Yansandan NajeriyaNijar ta amince da kundin ayyukan AES na shekara ta biyuAtiku ya zargi gwamnatin Tinubu da yi wa dimokuraɗiyya zagon ƙasaGwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanci
X whatsapp