Home Labarai Sojojin Najeriya biyar sun mutu a haɗarin mota a jihar Filato

Sojojin Najeriya biyar sun mutu a haɗarin mota a jihar Filato

Wasu sojojin sama na Najeriya biyar na daga cikin matafiya 19 da suka rasu a wani mummunan haɗarin mota da ya auku a Hawan Kibo da ke ƙaramar hukumar Riyom ta jihar Filato a jiya Talata.

A wata sanarwa da kakakin rundunar sojin sama ta Najeriya, Olusola Akinboyewa ya fitar, ya ce, sojojin na kan hanyarsu ne ta zuwa wani wasa a Abuja, lokacin da motarsu ta yi taho-mu-gama da wata babbar mota.

Sai dai kuma wani bayani da hukumar kiyaye haɗura ta Najeriya ta fitar ya saɓa da wanda kakakin sojin ya fitar, inda hukumar ta ce motar bas ta sojojin ƙirar Hiace, mai ɗaukar mutum 18 da ta taso daga Yola ta bi yo ta Jos a kan hanyarta ta zuwa Abuja ta ci karo ne da tirela wadda ke tsaye a kan hanya, lamarin da ya janyo mutuwar direban da dukkanin sauran mutanen da ke cikin motar su 18.

A wata hira da tasahar talabijin ta Channels, kakakin hukumar ta kiyaye haɗura (FRSC) a jihar ta Filato, Peter Longsan, ya ce dukkanin mutanen da ke cikin wannan mota bas da sojojin suke sun mutu.

Longsan ya danganta munin haɗarin da ya kai ga mutuwar mutanen gaba ɗaya, da gudun da direab bas ke yi inda ya ce a dalilin hakan ne da ta yi karo da tirelar ba wanda ya tsira.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com
Latest News
Gwamnatin Kano ta fara tantance ’yan kasuwa da gobarar Singer ta shafa don rabon tallafiSojojin Nijeriya sun kashe Kwamandan Boko haram da mai sayar Musu da jirgin Drone a AdamawaHisbah ta kama mutum tara saboda rashin yin azumi a KanoMajalisar jihar Rivers ta dakatar da shirin tsige FubaraMasu haƙar ma’adinai 33 sun mutu sakamakon gubar sinadarin carbon a FilatoSojojin Amurka 100 sun fara aikin horar da Sojin Najeriya don yaƙi da ta'addanciGwamnatin Najeriya da gwamnonin APC sun bai wa ƴan kasuwar Singer tallafin biliyan 8Kwankwasiyya ta yi martani kan matakin majalisar Amurka na hukunta KwankwasoSojojin Najeriya sun daƙile hare-haren mayaƙan ISWAP a BornoFarfesa Abdullahi Pakistan ya bayyana dalilinsa na ajiye shugaban Hukumar NAHCONMajalisar Najeriya ta kafa kwamitin nazari kan gyaran dokar zaɓeRundunar sojin Najeriya ta tura dakaru na musamman zuwa Filato don daƙile ƴanbindigaMajalisar Dinkin Duniya da Turkiya sun yi Alla-wadai da harin da aka kai KwaraAmurka ka iya sake kai Hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci- TrumpAmurka ka iya sake kai hari Nijeriya muddin aka ci gaba da kashe kiristoci
X whatsapp